A shekarun baya bayan nan gwamnatin kasar Sin na kara fadada manufofin shigo da hajoji daga ketare. Kuma mahukuntan kasar sun sha nanata cewa, hakan na nufin wanzar da matakai na kara rungumar sassan kasa da kasa, musamman ma kasashe masu tasowa a fannin ingiza samar da ci gaban bai daya.
Shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar karo na 15 da kasar Sin ta fara aiwatarwa, tun daga shekarar nan ta 2026 zuwa 2030, ya tanadi fadada kara bude kofar kasar bisa inganci, da goyon bayan daidaita tafarkin ci gaba a fannin shige da ficen hajoji tsakanin Sin da sauran kasashen duniya, kana da inganta rawar da dandalolin kasar masu bunkasa cinikayya ke takawa.
Karkashin hakan ne ma a ranar 4 ga watan Nuwamban 2025, Sin ta kaddamar da shirin musamman mai taken “Babbar kasuwa ga kowa: Shigar da hajoji cikin kasar Sin”, wanda ya kunshi jerin matakai na bunkasa hada-hadar shigar da kayayyakin kasashen duniya cikin babbar kasuwar Sin mai yalwa.
Ko shakka babu, wannan manufa ta sake tabbatar da aniyar kasar Sin ta raba damarmakinta na ci gaba tare da sauran sassan kasa da kasa ta hanyar bude kofofinta, da neman cimma moriyar bai daya, da raya hadin gwiwa mai nagarta, da ingiza tsarin dunkule tattalin arzikin duniya mai samar da alfanu ga dukkanin sassa, da gina al’umma mai makomar bai daya ga dukkanin bil’adama.
A gabar da wasu sassan duniya ke kara daukar matakan kashin kai, da baiwa kasuwa kariya, musamman ta kakaba tarin harajin fito, da sauran nau’o’in tarnaki, wanda ke haifarwa tsarin cinikayyar kasa da kasa mummunan tarnaki, da koma bayan hada-hada ga kasashe masu tasowa, kasar Sin a nata bangare ta yi nisa wajen kaddamar da manufofi daban daban wanda suka sabawa hakan, ciki har da kara fadada hajojin sassan ketare da take baiwa damar shigar su babbar kasuwarta, da goyon bayan karin daidaiton cinikayya.
Shaidu na hakika na nuna cewa, kasar Sin za ta ci gaba da ingiza bude kofa ga duniya, da mara baya ga tsarin cudanyar mabambantan sassa, da kara samar da gudunmawa ga gina tsarin bude tattalin arzikin duniya mai nagarta. Kuma yayin da take aiwatar da hakan, sassan kasa da kasa za su ci babbar gajiya daga yanayi na daidaituwar tattalin arzikin duniya.
Fatan dai shi ne sassan kasa da kasa za su rungumi sabbin damarmakin dake kunshe cikin manufar “Shigar da hajoji cikin kasar Sin”, kana za su shiga a dama da su a babbar kasuwar kasar, tare da amfana daga tarin alherai na bai daya wadanda kowa zai iya samu daga manufofin. (Saminu Alhassan)














