ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yakin Amurka/Israila Da Iran: Bukatar Takin Urea Ya Yi Matukar Karuwa

by Abubakar Abba and Sulaiman
6 months ago
Iran

Yakin da ake ci gaba da gwabzawa tsakanin Kasar Iran da Kasashen Isara’ila da Amurka, ya yi sanadiyyar karuwar bukatar Takin Zamani, musamman na Urea.

Yakin dai, ya shafi kasuwannin duniya wajen samar da Takin na Urea, musamman duba da cewa; yakin ya sanya wasu kasashen duniya, na ta faman kai komo na son samun Takin Urea, domin shirin fara noman bana.

Kazalika, yakin ya kuma yi sanadiyar rufe babbar mashigar Hormuz tare da kuma rufe masana’antun da ake sarrafa Takin Zamani a yankin Gulfda da kuma sauran wasu manyan hanyoyin da ake yin amfani da su wajen safarar Takin na Urea.

ADVERTISEMENT

Babbar mashigar ta Hormuz, ba wai kawai ana yin amfani da ita wajen safarar danyen mai ba ne, har da ma hada-hadar safarar Takin Zamani a duniya.

A cewar wani ma’aikaci a masana’antar sarrafa Takin Zamani ta Indorama, “Tun bayan da aka fara yakin, muna ci gaba da ganin karin bukatar ta Takin na Urea,”.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Ma’aikacin ya kara da cewa, amma muna mayar yin duba ne a kan abokan cinikinmu, kafin mu amshi bukatarsu ta Takin Zamani.

Ana sa ran wannan bukatar ta Takin na Urea, zai kara bunkasa kudaden shiga na Takin da aka fitar daga cikin kasar zuwa ketare, musamman ganin cewa; akwai dimbin irin wannan Taki a kasar.

A kasar nan dai, akwai masana’antu guda uku da suka yi fice, wadanda suka hada da Notore, Indorama da kuma ta Dangote, wadanda daukacinsu ke sarrafa Takin Zamanin da yawansa ya kai kimanin tan miliyan 6.5.

Misali, a shekarar 2023, wadannan masana’antu sun samar da kimanin tan miliyan 3.65 na Takin na Urea.

Kasancewar Gas shi ne jigo da ake yin amfani da shi wajen sarrafa sinadaran ammonia da na nitrogen da ake hada Takin na Urea, tun bayan fara yakin farashin sa a Tarayyar Turai, ya karu da kashi 50 cikin dari.

Hakan ya tilastawa manyan masu sarrafa Takin na Urea a Gabas ta Tsakiya, suka rage yawan adadin Takin na Urea da suke sarrafawa.

A cewar kafar yada labarai ta Bloomberg, sakamakon wannan tsadar farashi na Gas a kasuwar duniya, hatta babbar masana’antar sarrafa Takin Zamani da ke Kasar Slobakiya, ita ma ta sanar da rage yawan adadin Takin Zamanin da take samarwa.

A cewar tsohon sakataren kungiyar masu sarrafawa da kuma rabar da Takin Zamani na kasa, Gideon Negedu, an samu raguwar bukatar sinadarin hada Takin Zamani na ammonia da nitrogen da kuma na Urea, wadanda kuma dukkaninsu kasar nan na samar da su.

Ya bayyana cewa, a yanzu ana ci gaba da nuna bukatar Takin na Urea, da masana’antun cikin kasar ke samarwa, wanda kuma dole ne a kara zagewa, wajen kara mayar da hankali wajen sarrafa shi, domin a cike gurbin bukatar da ake da ita ta Takin na Urea.

Kazalika, kafar yada labarai ta Bloomberg, ta ruwaito mataimakin shugaban rukunonin kamfnin Dangote, Debakumar Edwin, ya sanar da cewa; kamfanin na ci gaba da samun karin bukatar ta Takin na Urea, musamman daga kasuwar duniya

“Bukatar ta Takin na Urea, ta karu daga kasuwar duniya saboda karancinsa da ake da shi a kasuwar duniya,” in ji Edwin.

Bugu da kari, ana sa ran wannan bukatar da ake da ita ta Takin na Urea a kasuwar duniya, za ta kara habaka hada-hadar fitar da kaya daga cikin kasar nan zuwa kasashen ketare.

A cewar wasu alkaluma da sashen hada-hadar kasuwanci a majalisar dinkin duniya ya fitar, a shekarar 2024 kacal, Nijeriya ta samu ribar kimanin dala miliyan 850 daga Takin Urea da fitar zuwa ketare.

Haka zalika, wannan alkaluma sun kuma nuna cewa; duk a shekarar ta 2024, Nijeriya ta fitar tan miliyan 3.2 na Takin na Urea zuwa kasuwar duniya.

Farashin Buhun Takin na Urea mai nauyin kilo 50 a cikin kasar nan 11 ya karu da kashi 11 a cikin dari, wato daga naira 33,000 zuwa Naira 36,500 kan farashin da aka sayar a makon da ya gabata.

Hakan na kuma kara jefa fargaba a zukatan al’ummar da ke fadin kasar nan, wadda ake yi wa lakabi da mafi yawan al’umma na nahiyar Afirka.

Iran
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood
Iran
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
An Yi Taro Kan Cinikayya Tsakanin Sin Da Afrika Ta Kudu Domin Zurfafa Hadin Gwiwa

An Yi Taro Kan Cinikayya Tsakanin Sin Da Afrika Ta Kudu Domin Zurfafa Hadin Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.