ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yakin Amurka/Israila Da Iran: Bukatar Takin Urea Ya Yi Matukar Karuwa

by Abubakar Abba and Sulaiman
2 months ago
Iran

Yakin da ake ci gaba da gwabzawa tsakanin Kasar Iran da Kasashen Isara’ila da Amurka, ya yi sanadiyyar karuwar bukatar Takin Zamani, musamman na Urea.

Yakin dai, ya shafi kasuwannin duniya wajen samar da Takin na Urea, musamman duba da cewa; yakin ya sanya wasu kasashen duniya, na ta faman kai komo na son samun Takin Urea, domin shirin fara noman bana.

Kazalika, yakin ya kuma yi sanadiyar rufe babbar mashigar Hormuz tare da kuma rufe masana’antun da ake sarrafa Takin Zamani a yankin Gulfda da kuma sauran wasu manyan hanyoyin da ake yin amfani da su wajen safarar Takin na Urea.

ADVERTISEMENT

Babbar mashigar ta Hormuz, ba wai kawai ana yin amfani da ita wajen safarar danyen mai ba ne, har da ma hada-hadar safarar Takin Zamani a duniya.

A cewar wani ma’aikaci a masana’antar sarrafa Takin Zamani ta Indorama, “Tun bayan da aka fara yakin, muna ci gaba da ganin karin bukatar ta Takin na Urea,”.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Ma’aikacin ya kara da cewa, amma muna mayar yin duba ne a kan abokan cinikinmu, kafin mu amshi bukatarsu ta Takin Zamani.

Ana sa ran wannan bukatar ta Takin na Urea, zai kara bunkasa kudaden shiga na Takin da aka fitar daga cikin kasar zuwa ketare, musamman ganin cewa; akwai dimbin irin wannan Taki a kasar.

A kasar nan dai, akwai masana’antu guda uku da suka yi fice, wadanda suka hada da Notore, Indorama da kuma ta Dangote, wadanda daukacinsu ke sarrafa Takin Zamanin da yawansa ya kai kimanin tan miliyan 6.5.

Misali, a shekarar 2023, wadannan masana’antu sun samar da kimanin tan miliyan 3.65 na Takin na Urea.

Kasancewar Gas shi ne jigo da ake yin amfani da shi wajen sarrafa sinadaran ammonia da na nitrogen da ake hada Takin na Urea, tun bayan fara yakin farashin sa a Tarayyar Turai, ya karu da kashi 50 cikin dari.

Hakan ya tilastawa manyan masu sarrafa Takin na Urea a Gabas ta Tsakiya, suka rage yawan adadin Takin na Urea da suke sarrafawa.

A cewar kafar yada labarai ta Bloomberg, sakamakon wannan tsadar farashi na Gas a kasuwar duniya, hatta babbar masana’antar sarrafa Takin Zamani da ke Kasar Slobakiya, ita ma ta sanar da rage yawan adadin Takin Zamanin da take samarwa.

A cewar tsohon sakataren kungiyar masu sarrafawa da kuma rabar da Takin Zamani na kasa, Gideon Negedu, an samu raguwar bukatar sinadarin hada Takin Zamani na ammonia da nitrogen da kuma na Urea, wadanda kuma dukkaninsu kasar nan na samar da su.

Ya bayyana cewa, a yanzu ana ci gaba da nuna bukatar Takin na Urea, da masana’antun cikin kasar ke samarwa, wanda kuma dole ne a kara zagewa, wajen kara mayar da hankali wajen sarrafa shi, domin a cike gurbin bukatar da ake da ita ta Takin na Urea.

Kazalika, kafar yada labarai ta Bloomberg, ta ruwaito mataimakin shugaban rukunonin kamfnin Dangote, Debakumar Edwin, ya sanar da cewa; kamfanin na ci gaba da samun karin bukatar ta Takin na Urea, musamman daga kasuwar duniya

“Bukatar ta Takin na Urea, ta karu daga kasuwar duniya saboda karancinsa da ake da shi a kasuwar duniya,” in ji Edwin.

Bugu da kari, ana sa ran wannan bukatar da ake da ita ta Takin na Urea a kasuwar duniya, za ta kara habaka hada-hadar fitar da kaya daga cikin kasar nan zuwa kasashen ketare.

A cewar wasu alkaluma da sashen hada-hadar kasuwanci a majalisar dinkin duniya ya fitar, a shekarar 2024 kacal, Nijeriya ta samu ribar kimanin dala miliyan 850 daga Takin Urea da fitar zuwa ketare.

Haka zalika, wannan alkaluma sun kuma nuna cewa; duk a shekarar ta 2024, Nijeriya ta fitar tan miliyan 3.2 na Takin na Urea zuwa kasuwar duniya.

Farashin Buhun Takin na Urea mai nauyin kilo 50 a cikin kasar nan 11 ya karu da kashi 11 a cikin dari, wato daga naira 33,000 zuwa Naira 36,500 kan farashin da aka sayar a makon da ya gabata.

Hakan na kuma kara jefa fargaba a zukatan al’ummar da ke fadin kasar nan, wadda ake yi wa lakabi da mafi yawan al’umma na nahiyar Afirka.

Iran
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 
Iran
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
An Yi Taro Kan Cinikayya Tsakanin Sin Da Afrika Ta Kudu Domin Zurfafa Hadin Gwiwa

An Yi Taro Kan Cinikayya Tsakanin Sin Da Afrika Ta Kudu Domin Zurfafa Hadin Gwiwa

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.