ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yakin Amurka/Israila Da Iran: Bukatar Takin Urea Ya Yi Matukar Karuwa

by Abubakar Abba and Sulaiman
3 months ago
Iran

Yakin da ake ci gaba da gwabzawa tsakanin Kasar Iran da Kasashen Isara’ila da Amurka, ya yi sanadiyyar karuwar bukatar Takin Zamani, musamman na Urea.

Yakin dai, ya shafi kasuwannin duniya wajen samar da Takin na Urea, musamman duba da cewa; yakin ya sanya wasu kasashen duniya, na ta faman kai komo na son samun Takin Urea, domin shirin fara noman bana.

Kazalika, yakin ya kuma yi sanadiyar rufe babbar mashigar Hormuz tare da kuma rufe masana’antun da ake sarrafa Takin Zamani a yankin Gulfda da kuma sauran wasu manyan hanyoyin da ake yin amfani da su wajen safarar Takin na Urea.

ADVERTISEMENT

Babbar mashigar ta Hormuz, ba wai kawai ana yin amfani da ita wajen safarar danyen mai ba ne, har da ma hada-hadar safarar Takin Zamani a duniya.

A cewar wani ma’aikaci a masana’antar sarrafa Takin Zamani ta Indorama, “Tun bayan da aka fara yakin, muna ci gaba da ganin karin bukatar ta Takin na Urea,”.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Ma’aikacin ya kara da cewa, amma muna mayar yin duba ne a kan abokan cinikinmu, kafin mu amshi bukatarsu ta Takin Zamani.

Ana sa ran wannan bukatar ta Takin na Urea, zai kara bunkasa kudaden shiga na Takin da aka fitar daga cikin kasar zuwa ketare, musamman ganin cewa; akwai dimbin irin wannan Taki a kasar.

A kasar nan dai, akwai masana’antu guda uku da suka yi fice, wadanda suka hada da Notore, Indorama da kuma ta Dangote, wadanda daukacinsu ke sarrafa Takin Zamanin da yawansa ya kai kimanin tan miliyan 6.5.

Misali, a shekarar 2023, wadannan masana’antu sun samar da kimanin tan miliyan 3.65 na Takin na Urea.

Kasancewar Gas shi ne jigo da ake yin amfani da shi wajen sarrafa sinadaran ammonia da na nitrogen da ake hada Takin na Urea, tun bayan fara yakin farashin sa a Tarayyar Turai, ya karu da kashi 50 cikin dari.

Hakan ya tilastawa manyan masu sarrafa Takin na Urea a Gabas ta Tsakiya, suka rage yawan adadin Takin na Urea da suke sarrafawa.

A cewar kafar yada labarai ta Bloomberg, sakamakon wannan tsadar farashi na Gas a kasuwar duniya, hatta babbar masana’antar sarrafa Takin Zamani da ke Kasar Slobakiya, ita ma ta sanar da rage yawan adadin Takin Zamanin da take samarwa.

A cewar tsohon sakataren kungiyar masu sarrafawa da kuma rabar da Takin Zamani na kasa, Gideon Negedu, an samu raguwar bukatar sinadarin hada Takin Zamani na ammonia da nitrogen da kuma na Urea, wadanda kuma dukkaninsu kasar nan na samar da su.

Ya bayyana cewa, a yanzu ana ci gaba da nuna bukatar Takin na Urea, da masana’antun cikin kasar ke samarwa, wanda kuma dole ne a kara zagewa, wajen kara mayar da hankali wajen sarrafa shi, domin a cike gurbin bukatar da ake da ita ta Takin na Urea.

Kazalika, kafar yada labarai ta Bloomberg, ta ruwaito mataimakin shugaban rukunonin kamfnin Dangote, Debakumar Edwin, ya sanar da cewa; kamfanin na ci gaba da samun karin bukatar ta Takin na Urea, musamman daga kasuwar duniya

“Bukatar ta Takin na Urea, ta karu daga kasuwar duniya saboda karancinsa da ake da shi a kasuwar duniya,” in ji Edwin.

Bugu da kari, ana sa ran wannan bukatar da ake da ita ta Takin na Urea a kasuwar duniya, za ta kara habaka hada-hadar fitar da kaya daga cikin kasar nan zuwa kasashen ketare.

A cewar wasu alkaluma da sashen hada-hadar kasuwanci a majalisar dinkin duniya ya fitar, a shekarar 2024 kacal, Nijeriya ta samu ribar kimanin dala miliyan 850 daga Takin Urea da fitar zuwa ketare.

Haka zalika, wannan alkaluma sun kuma nuna cewa; duk a shekarar ta 2024, Nijeriya ta fitar tan miliyan 3.2 na Takin na Urea zuwa kasuwar duniya.

Farashin Buhun Takin na Urea mai nauyin kilo 50 a cikin kasar nan 11 ya karu da kashi 11 a cikin dari, wato daga naira 33,000 zuwa Naira 36,500 kan farashin da aka sayar a makon da ya gabata.

Hakan na kuma kara jefa fargaba a zukatan al’ummar da ke fadin kasar nan, wadda ake yi wa lakabi da mafi yawan al’umma na nahiyar Afirka.

Iran
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware
Iran
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
An Yi Taro Kan Cinikayya Tsakanin Sin Da Afrika Ta Kudu Domin Zurfafa Hadin Gwiwa

An Yi Taro Kan Cinikayya Tsakanin Sin Da Afrika Ta Kudu Domin Zurfafa Hadin Gwiwa

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.