Mazauna garin Eda Oniyo da ke Jihar Ekiti, shalkwatar ƙaramar hukumar Ilejemeje, sun shiga cikin fargaba bayan wasu ‘yan bindiga sun kai hari kan al’ummar yankin, inda suka kashe mutum guda tare da sace wasu da dama.
Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya faru ne a yammacin ranar Talata, lokacin da ake gudanar da wani taron wa’azi a fili wanda wata coci ta shirya a yankin da misalin ƙarfe 7 na yamma.
An ce ‘yan bindigar sun riƙa harbe-harbe ba kakkautawa, inda suka kashe faston wanda shi ne baƙon da aka gayyata, sannan suka sace wasu daga cikin masu ibadar a yayin harin.
Wata majiya daga yankin ta bayyana cewa maharan, waɗanda ke ɗauke da muggan makamai, sun aikata abin da suka ga dama kafin su tsere da mutanen da suka sace zuwa cikin wani daji da ke kusa.
Wani jagoran al’umma, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya shaida wa manema labarai a Ado-Ekiti cewa daga cikin waɗanda aka sace akwai tsofaffi da yara.
A cewarsa, “Da yammacin yau, kafin ƙarfe bakwai kaɗan, ‘yan bindiga sun kai hari kan wani taron coci a Eda Oniyo. Sun harbe fasto tare da bude wuta kan masu ibada, suka kuma sace da dama ciki har da tsofaffi da yara, suka tafi da su cikin daji. Yawan maharan ya girgiza al’umma, kuma iyalai na ci gaba da neman ‘yan uwansu da suka ɓace.”
Shugaban ƙaramar hukumar Ilejemeje, Hon. Pius Alaba, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce rahotanni daga faston da ke kula da cocin sun nuna cewa sama da masu ibada 50 ne suka halarci taron, inda da dama daga cikinsu suka samu tserewa zuwa cikin daji.
Ya ƙara da cewa gawar faston baƙon, wanda aka ce daga wata jiha makwabta ya zo, an kai ta ɗakin ajiye gawa.















Discussion about this post