Wasu masu neman takarar gwamna a PDP guda hudu a jihar Gombe sun bayyana adawarsu ga wani zargin yunƙurin da tsohon ministan sadarwa da tattalin arziƙin zamani, Isa Ali Pantami, ke yi na komawa PDP domin shiga zaben fidda gwani na gwamna.
A cikin wata sanarwa da suka fitar tare, Abdulkadir Hamma Saleh, da Khamisu Ahmed Mailantarki, da Usman Aliyu Garry da Monica Kaltho sun yi gargaɗin cewa irin wannan mataki na iya jefa jam’iyyar cikin rikicin shari’a tare da kawo cikas ga tsarin cikin gida na jam’iyyar.
Masu neman takarar sun ce sun amince da bai wa shugabannin jam’iyyar damar zabar ɗan takarar sulhu daga cikinsu bayan tuntuɓa da shugabannin PDP na jihar ciki har da tsohon gwamna Ibrahim Hassan Dankwambo. Sun kuma ce sun rattaba hannu kan yarjejeniyar mutunta duk wata matsaya da jam’iyyar ta dauka.
Sai dai sun nuna damuwa kan rahotannin da ke cewa Isa Ali Pantami, wanda ake zargin ya shiga zaben fidda gwani na APC a ranar 21 ga Mayu, 2026, na neman komawa PDP domin sake shiga takara.
Masu neman takarar sun ce dokokin zaɓe da tsarin dimokuraɗiyya ba su amince mutum ya shiga zaben fidda gwani a jam’iyya biyu daban-daban a zagaye guda ba. Sun buƙaci shugabannin PDP da su kauce wa duk wani mataki da zai iya haifar da rabuwar kai ko kuma jefa jam’iyyar cikin matsalar shari’a kafin zaben 2027.















Discussion about this post