ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

’Yansanda Sun Ceto Wani Malamin Addini Da Matasa Suka Tsare A Jihar Gombe

by Rabi'u Ali Indabawa
4 months ago
Gombe

Jami’an  ‘yansanda a Jihar Gombe sun ceto wani malamin addini da wasu matasa suka kulle a cikin gida a kauyen Birin Fulani da ke Karamar Hukumar Nafada.

Rundunar ’yansandan jihar ta ce malamin, mai suna Abubakar Mahmoud Puma, mai shekaru 58 daga Karamar Hukumar Akko, an ceto shi cikin koshin lafiya bayan wasu matasa da ake zargin mambobin wata kungiya ne suka kulle shi a cikin wani gida.

  • Wang Yi Ya Zanta Ta Wayar Tarho Da Ministar Harkokin Wajen Birtaniya 
  • Aikin Zamantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya Zai Rage Wa Kasa Asasar Naira Tiriliyan Daya —Dantsoho

Kakakin rundunar ’yansandan jihar, DSP Buhari Abdullahi, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, lamarin ya faru ne da misalin karfe 3:00 na safiyar ranar 15 ga Maris, 2026, bayan rundunar ta samu rahoton tashin hankali a cikin al’ummar Birin Fulani.

“Ranar 15/03/2026 da misalin karfe 0300, rundunar ta samu rahoton tashin hankali da barazanar karya zaman lafiya a Birin Fulani da ke Karamar Hukumar Nafada,” in ji Abdullahi.

LABARAI MASU NASABA

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

Ya bayyana cewa jami’in ’yansandan yankin (DPO) ya gaggauta tura tawagar jami’ai zuwa wurin domin dawo da zaman lafiya.

“Da isarsu wurin, an gano cewa wani Abubakar Mahmoud Puma, mai shekaru 58 daga Karamar Hukumar Akko a Jihar Gombe, wasu fusatattun matasa sun kulle shi a cikin gida, bisa zargin cewa ya yi kalaman cin zarafi da batanci ga shugabanninsu,” in ji sanarwar.

Abdullahi ya kara da cewa an tura malamin zuwa yankin ne domin gudanar da Tafsir na watan Ramadan na shekarar 2026, wanda hedikwatar kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’a Wa Ikamatus Sunnah ta kasa da ke Jos ta tura shi.

Ya ce jami’in ’yansandan yankin ya tattauna da matasan da suka fusata, lamarin da ya kai ga ceto malamin lafiya.

“Jami’in ’yansandan yankin ya tattauna da matasan cikin hikima. Bayan wannan shiga tsakani, matasan suka ba da hadin kai, aka ceto malamin lafiya ba tare da ya ji rauni ba. Ba a rasa rai ba kuma an dawo da zaman lafiya a yankin,” in ji shi.

A halin yanzu, kwamishinan ’yansandan jihar, Umar Ahmed Chuso, ya ba da umarnin a gudanar da bincike a boye domin gano musabbabin faruwar lamarin.

“Kwamishinan ’yansandan ya ba da umarnin gudanar da cikakken bincike domin gano musabbabin da suka jawo faruwar lamarin da kuma tabbatar da cewa duk wanda aka samu da laifi ya fuskanci hukunci bisa doka,” in ji Abdullahi.

Rundunar ’yansandan ta kuma gargadi jama’a da su guji yada labaran karya ko wadanda ba a tabbatar da su ba a shafukan sada zumunta.

“Rundunar na jan hankalin jama’a da su guji wallafa ko yada labaran karya ko marasa tabbaci da ka iya haifar da tashin hankali ko rudar da jama’a,” in ji sanarwar.

Har ila yau, rundunar ta tabbatar wa mazauna Birin Fulani da ma daukacin Jihar Gombe cewa an shawo kan lamarin, tare da kira ga jama’a da su rika bin hanyoyin doka wajen gabatar da koke-kokensu maimakon daukar matakan da ka iya tayar da hankalin jama’a ko karya zaman lafiya.

Gombe
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sarkin Zazzau Ya Umarci A Soke Wasu Al’adu Da Ke Kawo Wa Aure Cikas

MASU ALAKA

Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Next Post
Tankar Mai Ta Yi Mummunan Hatsari A Kogi, Gwamnati Ta Ɗauki Mataki

Tankar Mai Ta Yi Mummunan Hatsari A Kogi, Gwamnati Ta Ɗauki Mataki

LABARAI MASU NASABA

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.