ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

’Yansanda Sun Ceto Wani Malamin Addini Da Matasa Suka Tsare A Jihar Gombe

by Rabi'u Ali Indabawa
3 months ago
Gombe

Jami’an  ‘yansanda a Jihar Gombe sun ceto wani malamin addini da wasu matasa suka kulle a cikin gida a kauyen Birin Fulani da ke Karamar Hukumar Nafada.

Rundunar ’yansandan jihar ta ce malamin, mai suna Abubakar Mahmoud Puma, mai shekaru 58 daga Karamar Hukumar Akko, an ceto shi cikin koshin lafiya bayan wasu matasa da ake zargin mambobin wata kungiya ne suka kulle shi a cikin wani gida.

  • Wang Yi Ya Zanta Ta Wayar Tarho Da Ministar Harkokin Wajen Birtaniya 
  • Aikin Zamantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya Zai Rage Wa Kasa Asasar Naira Tiriliyan Daya —Dantsoho

Kakakin rundunar ’yansandan jihar, DSP Buhari Abdullahi, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, lamarin ya faru ne da misalin karfe 3:00 na safiyar ranar 15 ga Maris, 2026, bayan rundunar ta samu rahoton tashin hankali a cikin al’ummar Birin Fulani.

“Ranar 15/03/2026 da misalin karfe 0300, rundunar ta samu rahoton tashin hankali da barazanar karya zaman lafiya a Birin Fulani da ke Karamar Hukumar Nafada,” in ji Abdullahi.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

Ya bayyana cewa jami’in ’yansandan yankin (DPO) ya gaggauta tura tawagar jami’ai zuwa wurin domin dawo da zaman lafiya.

“Da isarsu wurin, an gano cewa wani Abubakar Mahmoud Puma, mai shekaru 58 daga Karamar Hukumar Akko a Jihar Gombe, wasu fusatattun matasa sun kulle shi a cikin gida, bisa zargin cewa ya yi kalaman cin zarafi da batanci ga shugabanninsu,” in ji sanarwar.

Abdullahi ya kara da cewa an tura malamin zuwa yankin ne domin gudanar da Tafsir na watan Ramadan na shekarar 2026, wanda hedikwatar kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’a Wa Ikamatus Sunnah ta kasa da ke Jos ta tura shi.

Ya ce jami’in ’yansandan yankin ya tattauna da matasan da suka fusata, lamarin da ya kai ga ceto malamin lafiya.

“Jami’in ’yansandan yankin ya tattauna da matasan cikin hikima. Bayan wannan shiga tsakani, matasan suka ba da hadin kai, aka ceto malamin lafiya ba tare da ya ji rauni ba. Ba a rasa rai ba kuma an dawo da zaman lafiya a yankin,” in ji shi.

A halin yanzu, kwamishinan ’yansandan jihar, Umar Ahmed Chuso, ya ba da umarnin a gudanar da bincike a boye domin gano musabbabin faruwar lamarin.

“Kwamishinan ’yansandan ya ba da umarnin gudanar da cikakken bincike domin gano musabbabin da suka jawo faruwar lamarin da kuma tabbatar da cewa duk wanda aka samu da laifi ya fuskanci hukunci bisa doka,” in ji Abdullahi.

Rundunar ’yansandan ta kuma gargadi jama’a da su guji yada labaran karya ko wadanda ba a tabbatar da su ba a shafukan sada zumunta.

“Rundunar na jan hankalin jama’a da su guji wallafa ko yada labaran karya ko marasa tabbaci da ka iya haifar da tashin hankali ko rudar da jama’a,” in ji sanarwar.

Har ila yau, rundunar ta tabbatar wa mazauna Birin Fulani da ma daukacin Jihar Gombe cewa an shawo kan lamarin, tare da kira ga jama’a da su rika bin hanyoyin doka wajen gabatar da koke-kokensu maimakon daukar matakan da ka iya tayar da hankalin jama’a ko karya zaman lafiya.

Gombe
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Next Post
Tankar Mai Ta Yi Mummunan Hatsari A Kogi, Gwamnati Ta Ɗauki Mataki

Tankar Mai Ta Yi Mummunan Hatsari A Kogi, Gwamnati Ta Ɗauki Mataki

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.