ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

’Yansanda Sun Ceto Wani Malamin Addini Da Matasa Suka Tsare A Jihar Gombe

by Rabi'u Ali Indabawa
6 months ago
Gombe

Jami’an  ‘yansanda a Jihar Gombe sun ceto wani malamin addini da wasu matasa suka kulle a cikin gida a kauyen Birin Fulani da ke Karamar Hukumar Nafada.

Rundunar ’yansandan jihar ta ce malamin, mai suna Abubakar Mahmoud Puma, mai shekaru 58 daga Karamar Hukumar Akko, an ceto shi cikin koshin lafiya bayan wasu matasa da ake zargin mambobin wata kungiya ne suka kulle shi a cikin wani gida.

  • Wang Yi Ya Zanta Ta Wayar Tarho Da Ministar Harkokin Wajen Birtaniya 
  • Aikin Zamantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya Zai Rage Wa Kasa Asasar Naira Tiriliyan Daya —Dantsoho

Kakakin rundunar ’yansandan jihar, DSP Buhari Abdullahi, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, lamarin ya faru ne da misalin karfe 3:00 na safiyar ranar 15 ga Maris, 2026, bayan rundunar ta samu rahoton tashin hankali a cikin al’ummar Birin Fulani.

“Ranar 15/03/2026 da misalin karfe 0300, rundunar ta samu rahoton tashin hankali da barazanar karya zaman lafiya a Birin Fulani da ke Karamar Hukumar Nafada,” in ji Abdullahi.

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

Ya bayyana cewa jami’in ’yansandan yankin (DPO) ya gaggauta tura tawagar jami’ai zuwa wurin domin dawo da zaman lafiya.

“Da isarsu wurin, an gano cewa wani Abubakar Mahmoud Puma, mai shekaru 58 daga Karamar Hukumar Akko a Jihar Gombe, wasu fusatattun matasa sun kulle shi a cikin gida, bisa zargin cewa ya yi kalaman cin zarafi da batanci ga shugabanninsu,” in ji sanarwar.

Abdullahi ya kara da cewa an tura malamin zuwa yankin ne domin gudanar da Tafsir na watan Ramadan na shekarar 2026, wanda hedikwatar kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’a Wa Ikamatus Sunnah ta kasa da ke Jos ta tura shi.

Ya ce jami’in ’yansandan yankin ya tattauna da matasan da suka fusata, lamarin da ya kai ga ceto malamin lafiya.

“Jami’in ’yansandan yankin ya tattauna da matasan cikin hikima. Bayan wannan shiga tsakani, matasan suka ba da hadin kai, aka ceto malamin lafiya ba tare da ya ji rauni ba. Ba a rasa rai ba kuma an dawo da zaman lafiya a yankin,” in ji shi.

A halin yanzu, kwamishinan ’yansandan jihar, Umar Ahmed Chuso, ya ba da umarnin a gudanar da bincike a boye domin gano musabbabin faruwar lamarin.

“Kwamishinan ’yansandan ya ba da umarnin gudanar da cikakken bincike domin gano musabbabin da suka jawo faruwar lamarin da kuma tabbatar da cewa duk wanda aka samu da laifi ya fuskanci hukunci bisa doka,” in ji Abdullahi.

Rundunar ’yansandan ta kuma gargadi jama’a da su guji yada labaran karya ko wadanda ba a tabbatar da su ba a shafukan sada zumunta.

“Rundunar na jan hankalin jama’a da su guji wallafa ko yada labaran karya ko marasa tabbaci da ka iya haifar da tashin hankali ko rudar da jama’a,” in ji sanarwar.

Har ila yau, rundunar ta tabbatar wa mazauna Birin Fulani da ma daukacin Jihar Gombe cewa an shawo kan lamarin, tare da kira ga jama’a da su rika bin hanyoyin doka wajen gabatar da koke-kokensu maimakon daukar matakan da ka iya tayar da hankalin jama’a ko karya zaman lafiya.

Gombe
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Next Post
Tankar Mai Ta Yi Mummunan Hatsari A Kogi, Gwamnati Ta Ɗauki Mataki

Tankar Mai Ta Yi Mummunan Hatsari A Kogi, Gwamnati Ta Ɗauki Mataki

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.