• Leadership Hausa
Thursday, March 23, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Fitar Da Gwani A Jam’iyyar APC Ya Bar Baya Da Kura A Jihar Sakkwato

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
10 months ago
in Siyasa
0
Zaben Fitar Da Gwani A Jam’iyyar APC Ya Bar Baya Da Kura A Jihar Sakkwato
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan takara uku daga cikin ‘yan takarar Gwamnan Sakkwato a inuwar jam’iyyar APC sun sa kafa sun yi fatali da zaben fitar da gwani da aka gudanar kan abin da suka kira da tafka magudi wajen tantance wakilai masu zabe, a kan hakan suka sha alwashin kalubalantar zaben.

Dakta Kabir Dasuki, jigo a Jam’iyyar APC ne ya yi wannan Jawabin ga manema labarai a madadin ‘yan takara uku da aka yi galaba a kansu, wato Ambasada Faruku Malami Yabo, Jakadan Nijeriya a Kasar Jordan da Sanata Ibrahim Abdullahi Gobir wanda ke wakiltar Sakkwato ta Gabas a Majalisar Dattawa sai kuma Alhaji A.A Gumbi.

  • 2023: Jm’iyyar APC Ta Fara Tantance Masu Neman Takarar Shugabancin Nijeriya
  • 2023: Duk Sanatocin Bauchi Masu Ci Babu Mai Komawa Sun Sha Kaye A Mazabunsu

Ya ce ko kadan ba a bi ka’ida ba a zaben, an kuma tafka magudi don haka za su bi hakkinsu a duk inda ya kamata domin ba za su taba yadda da sabawa dokar zabe ba. Zaben da aka gudanar ba sahihi ba ne wanda kowane bangare zai iya yadda da shi ba.

“Tun daga wajen tantance deliget aka fara samun matsala, a inda za ka ga ejen din daya dan takarar, Ahmad Aliyu, da dan ubangidansa, Sanata Aliyu Wamakko a cikin mutanen da ke aikin tantance wakilai masu zabe. Kwamitin zaben da suka zo daga Abuja kawai sun zama ‘yan kallo ne kawai domin ‘yan gidan Wamakko ne suka karbe aikin tantancewar.” In ji shi.

Ya ce abin takaici ne deliget da wanda ya yi karatu da wanda bai yi karatu ba a ce duka sai dai a rubuta masu wanda za su zaba. Haka ma ya ce ana cikin zabe wutar janareta ta yi ta daukewa, aka zauna cikin duhu tare da yin abin da aka ga dama, wanda akan wadannan abubuwan ya ce za su bi hakkinsu a duk inda ya kamata.

Labarai Masu Nasaba

Jihar Zamfara: Dauda Lawal Dare Na Jam’iyyar PDP Ya Kayar Da Gwamna Matawalle Na APC

PDP Na Zargin Gwamnan Zamfara Da Yunkurin Murde Sakamakon Karamar Hukumar Maradun

Tags: SakkwatoZaben Fidsa Gwani
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Sako Wasu Mutum 2 Da Suka Sace A Wata Cocin Jihar Abiya 

Next Post

Ina Fata Deliget Ku Zabe Ni Ranar Zaben Fitar Da Gwani Ko Ban Baku Ko Sisi Ba —Badaru

Related

Jihar Zamfara: Dauda Lawal Dare Na Jam’iyyar PDP Ya Kayar Da Gwamna Matawalle Na APC
Siyasa

Jihar Zamfara: Dauda Lawal Dare Na Jam’iyyar PDP Ya Kayar Da Gwamna Matawalle Na APC

3 days ago
Babban Kwamatin Ayyuka Na Jam’iyyar PDP Na kasa Ya Gana Da ‘Yan Takarar Gwamna Na Jam’iyyar
Siyasa

PDP Na Zargin Gwamnan Zamfara Da Yunkurin Murde Sakamakon Karamar Hukumar Maradun

3 days ago
Da Dumi-Dumi: INEC Ta Ce Sakamakon Zaben Gwamnan Kebbi Bai Kammalu Ba
Siyasa

Da Dumi-Dumi: INEC Ta Ce Sakamakon Zaben Gwamnan Kebbi Bai Kammalu Ba

4 days ago
Dan Takarar PDP, Hon. Dauda Lawal Shi Ne A Gaba A Zaben Gwamnan Zamfara
Siyasa

Dan Takarar PDP, Hon. Dauda Lawal Shi Ne A Gaba A Zaben Gwamnan Zamfara

4 days ago
Dogara Ya Mara Wa Dan Takarar Gwamnan APC A Bauchi Baya
Siyasa

Dogara Ya Mara Wa Dan Takarar Gwamnan APC A Bauchi Baya

2 weeks ago
Rikicin PDP: Bayan Ganawar Tinubu Da Wike A Landan, Ba Shiri Atiku Ya Garzaya Birtaniya
Siyasa

Wike Ya Yi Wa Atiku Shagube Kan Zanga-Zangar Neman INEC Ta Soke Zaben Shugaban Kasa

2 weeks ago
Next Post
Ina Fata Deliget Ku Zabe Ni Ranar Zaben Fitar Da Gwani Ko Ban Baku Ko Sisi Ba —Badaru

Ina Fata Deliget Ku Zabe Ni Ranar Zaben Fitar Da Gwani Ko Ban Baku Ko Sisi Ba —Badaru

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Dokokin Kogi Ta Dakatar Da ‘Yan Majalisa 9 D Wasu Kan Zargin Ta’addanci

Majalisar Dokokin Kogi Ta Dakatar Da ‘Yan Majalisa 9 D Wasu Kan Zargin Ta’addanci

March 23, 2023
An Yaba Da Yadda Tawagar Likitocin Kasar Sin Ta Ba Da Hidimar Kiwon Lafiya A Sudan Ta Kudu

An Yaba Da Yadda Tawagar Likitocin Kasar Sin Ta Ba Da Hidimar Kiwon Lafiya A Sudan Ta Kudu

March 23, 2023
Xi Jinping Ya Kammala Ziyararsa A Kasar Rasha Cikin Nasara

Xi Jinping Ya Kammala Ziyararsa A Kasar Rasha Cikin Nasara

March 23, 2023
Matawalle Ya Karbi Faduwa, Ya Yi Fatan Alheri Ga Sabon Gwamnan Zamfara

Matawalle Ya Karbi Faduwa, Ya Yi Fatan Alheri Ga Sabon Gwamnan Zamfara

March 23, 2023
Siyasantar Da Batun Gano Asalin COVID-19 Dabara Ce Ta Boye Gaskiya

Siyasantar Da Batun Gano Asalin COVID-19 Dabara Ce Ta Boye Gaskiya

March 23, 2023
Jirgin Saman Nijeriya Zai Fara Aiki Kafin Ranar 29 Ga Mayu

Jirgin Saman Nijeriya Zai Fara Aiki Kafin Ranar 29 Ga Mayu

March 23, 2023
Ina So A Ko’ina A Ji Hikima Da Fasaharmu – Yusuf King

Ina So A Ko’ina A Ji Hikima Da Fasaharmu – Yusuf King

March 23, 2023
Hadin Gwiwar Sin Da Rasha Na Da Muhimmanci Sosai Ga Duniya

Hadin Gwiwar Sin Da Rasha Na Da Muhimmanci Sosai Ga Duniya

March 23, 2023
Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumin Gobe A Wasu Birane

Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumin Gobe A Wasu Birane

March 23, 2023
Gyare-gyare Su Kan Faru Ne Bisa Sauyawar Tunanin Mutum

Gyare-gyare Su Kan Faru Ne Bisa Sauyawar Tunanin Mutum

March 23, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.