Mazauna ƙauyen Gurbi da ke ƙaramar hukumar Kankara a jihar Katsina sun daƙile yunƙurin hare-haren ‘yan bindiga, bayan sun haɗa kai domin kare al’ummarsu.
Wani mazaunin yankin ya bayyana cewa maharan sun iso da yamma, amma ba su samu damar shiga ƙauyen ba, domin jama’a sun taru suka tare musu hanya. Sai dai duk da haka, rahotanni sun nuna cewa sama da mutane 10 sun rasa rayukansu a yankin Nagoɗi, wani ƙauye da ke kusa da Gurbi.
Majiyar ta ƙara da cewa mazaunan sun sanar da jami’an tsaro tun da farko bayan samun bayanan sirri kan yiwuwar harin, amma ba a samu martani ko ɗauki ba sai bayan an kai harin. Daga baya ne jami’an tsaro suka iso suka kwashe gawarwaki.
Daily Trust ta rawaito cewa; wata majiya ta kusa da fadar shugaban ƙauyen ta tabbatar da cewa ‘yan bindigar ba su samu shiga Gurbi ba, sai dai sun kai hari kan wasu da suka yi yunƙurin tserewa. Wannan na zuwa ne yayin da Kankara ke fuskantar ƙaruwar hare-haren ‘yan bindiga a ‘yan kwanakin nan.















Discussion about this post