Aƙalla mutane bakwai ne aka bayyana sun ɓace bayan wata mummunar gobara da ta tashi a Kasuwar Singa da ke Jihar Kano. Shugaban Ci Gaban Kasuwar Sings (SIMDA), Barrista Junaidu M. Zakari, ya shaida wa manema labarai cewa har yanzu ba a gano inda mutanen suke ba, yayin da ake ci gaba da bincike domin tabbatar da ko suna raye ko a’a.
Zakari ya ce gobarar ta lalata kadarori da darajarsu ta haura Naira biliyan 5, yana mai bayyana lamarin a matsayin ɗaya daga cikin mafi muni a tarihin kasuwar. Ya ƙara da cewa wutar ta ƙone gidaje huɗu da ke ɗauke da dubban ƙananan rumfunan ’yan kasuwa, tare da lalata kayayyaki da kayan aiki da suka kasance tushen rayuwar ɗaruruwan iyalai.
- Gobara Ta Sake Tashi A Kasuwar Singa A Kano
- Sin Ta Mika Sakon Ta’azziya Sakamakon Gobara Da Ta Kone Wani Babban Kanti A Pakistan
Wani jami’in kasuwar, Ibrahim, ya ce gobarar ta ƙone sama da shaguna 100 da kuma rumbuna fiye da 50, inda wasu daga cikinsu ke ɗauke da kayayyakin da darajarsu ta kai miliyoyin Naira. Ya ce wutar ta ci gaba da ci har tsawon dare, kuma ana zargin na’urorin samar da wuta mai amfani da hasken rana (solar panel) na iya kasancewa sanadin tashin gobarar.
Shugaban SIMDA ya ce jami’an agajin gaggawa da hukumomin tsaro na ci gaba da bincike domin gano musabbabin gobarar. Ya kuma yaba wa gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, bisa ziyarar da ya kai wurin yayin da gobarar ke ci, yana mai cewa hakan ya nuna tausayi da goyon baya ga waɗanda abin ya shafa.
Har yanzu hukumomi ba su fitar da sakamakon bincike kan musabbabin gobarar ba, yayin da ’yan kasuwa ke ƙoƙarin kwashe abin da ya rage daga dukiyoyinsu, tare da kira ga gwamnati da masu ruwa da tsaki su tallafa musu domin farfaɗo da kasuwancinsu.














Discussion about this post