Wasu da ake zargin mayaƙan Boko Haram ne sun kai hari kan ayarin motocin ɗan takarar gwamnan Jihar Borno na jam’iyyar APC, Mustapha Gubio, a kan hanyar Gubio–Kareto–Damasak a arewacin jihar. Lamarin ya faru ne a ranar Alhamis, yayin da Gubio da tawagarsa ke kan hanyar zuwa Mobbar domin yi wa magoya bayan APC godiya bayan samun tikitin takarar jam’iyyar.
Majiyoyi sun ce ‘yan ta’addan sun buɗe wa ayarin wuta da makamai masu linzami da harbin bindigogi da misalin karfe 2:30 na rana a kusa da garin Kareto. Sai dai jami’an tsaro da suka haɗa da sojoji, ‘yansanda, da NSCDC, da DSS, da CJTF da jami’an sa-kai sun yi gaggawar mayar da martani tare da fatattakar maharan.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansanda, Ani Iniedu, ya tabbatar da harin, inda ya ce jami’an tsaro sun yi arangama da maharan bayan sun kai hari da IED da makaman roka. Ya ce an tilasta wa maharan komawa cikin daji, sannan jami’an tsaro suka binciki yankin domin tabbatar da babu wasu abubuwan fashewa da suka rage.
An ce an yi wa wasu motocin ‘yansanda masu sulke ɓarna sakamakon harin, amma babu wani rahoton rasa rai daga cikin tawagar Gubio. Rundunar ‘yansanda ta ce an kwashe ɗan takarar da sauran jami’an gwamnati da ‘yan siyasar da ke cikin ayarin zuwa wani wuri mai tsaro.
Harin ya ƙara nuna ƙalubalen tsaro da ke ci gaba da fuskantar sassan arewacin Jihar Borno, musamman yankunan da ke kan iyaka da tafkin Chadi, yayin da jami’an tsaro ke ci gaba da gudanar da ayyukan daƙile ayyukan ƙungiyoyin ‘yan ta’adda a yankin.














