Jami’an rundunar ‘yansandan Abuja sun daƙile wani yunƙurin garkuwa da wasu ma’aurata a yankin Byazhin da ke Abuja, bayan fafatawa da suka yi da waɗanda ake zargin masu garkuwa da mutane ne.
A yayin farmakin, jami’an sun ƙwato bindigar AK-47 guda ɗaya, da sinƙin harsasai da kuma harsasai bakwai.
Kakakin rundunar, SP Josephine Adeh, ta ce jami’an sashin yaƙi da garkuwa da mutane sun samu bayanan sirri kan motsin wasu da ake zargi a kusa da yankin Redeemed Church da ke Byazhin.
Da isarsu wurin da misalin ƙarfe 12:34 na dare, sun tarar da maharan na ƙoƙarin shiga wani gida ta ƙarfi da yaji domin yin garkuwa da mazaunansa.
Ta ce da maharan suka hango jami’an tsaro sai suka buɗe musu wuta, lamarin da ya haddasa musayar harbi na sama da mintuna 30. Daga bisani jami’an suka fatattaki maharan, waɗanda suka tsere cikin daji ɗauke da raunukan harbin bindiga.
An ceto ma’auratan da aka bayyana sunayensu da Mista Samson da matarsa ba tare da sun ji rauni ba.
Daga bisani an kai su Asibitin Gwarinpa domin kula da lafiyarsu, yayin da Kwamishinan ‘Yansanda na FCT, CP Ahmed Muhammed Sanusi, ya yaba wa jami’an tare da umartar ƙara tsaurara sintiri da matakan tsaro a yankin.















Discussion about this post