ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: An Bukaci ‘Yan Takara Su Yi Koyi Da Manufofin Yariman Bakura — Onaiyekan

by Muhammad
4 years ago
2023

A ci gaba da tuntubar kungiyoyi da shugabannin Addinai da tsohon gwamnan Jihar Zamfara kuma daya daga cikin masu takarar shugaban kasa a karkashin Jam’iyyar APC, Sanata Ahmad Rufa’i Sani Yarima, yake yi.2023

Sanata Yarima ya ziyarci babban malamin Coci kuma shugaban gidauniyar wanzar da zaman lafiya, John Cardinal O. Onaiyekan a gidansa da ke Abuja don sanar da shi kudurinsa na takarar shugaban kasa a Jam’iyyar APC da neman tabarraki da addu’a da tabbatar da niyyarsa ta samar da zaman lafiya a Nijeriya.

  • Babu wata Yarjejeniya Da Aka Gindaya Cewa Za A Ba Tinubu Shugaban Kasa Bayan Buhari -Yerima
  • 2023: Yarima Ne Kadai Zai Iya Dorawa Da Irin Nasarar Da Buhari Ya Samu A Mulki —Olumide

Yarima ya ce, kirkiro ma’aikatar kula da harkokin Addinai a Nijeriya zai taimaka wurin samar da zaman lafiya tsakanin mabiya addinai a Nijeriya2023

ADVERTISEMENT

Ahmad Yerima ya tabbatar da cewa a burinsa na ceto Nijeriya da kuma matsayinsa na dan Jam’iyyar APC mai biyayya, zai goyi bayan duk wanda Jam’iyyar ta tsayar a matsayin dan takararta ko da kuwa shi bai samu nasara zama dan takarar Jam’iyyar ba.

Sanata Yarima ya ce dukda cewa mai alfarma Sarkin Musulmi na jagorantar majalisar addinai kuma suna kokari, dukda haka akwai bukatar a samu fiye da haka, ” Yana da kyau a samu ma’aikata ta musanman da zata kula da harkokin addinai da zata kula da lamuran Musulmi da Kiristoci a Nijeriya, wannan na cikin kunshin kudurinmu cikin ikon Allah da zarar mun yi nasara a 2023” Cewar Yarima.

LABARAI MASU NASABA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

A nasa jawabin babban malamin cocin, John Cardinal Onaiyekan, ya ce kowane dan adam yana iya bakin kokarinsa kan neman bukatarsa sai da kuma Allah ne mafi sanin waye zai zama shugban Nijeriya a gobe cikin dubban maza da mata da muke da su.

Bishop Onaiyekan ya ce, “Zan ci gaba da yi maka Addu’a da neman Allah ya ci gaba da shiga lamuranka a cikin wannan gwagwarmaya”.

Onaiyekan, ya bukaci sauran jagororin Siyasa da masu muradin tsayawa takara da su yi koyi da salon Ahmad Sani Yarima, ta yadda za su samu hasken damar shugabancin Nijeriya cikin dafawar ubangiji.

A yayin ziyarar Sanata Yerima yana tare da dawagar yakin neman zabensa.

2023
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano

MASU ALAKA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna
Siyasa

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

September 9, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Next Post
Manyan Kurakuran Iyaye Wajen Tarbiyya (II)

Manyan Kurakuran Iyaye Wajen Tarbiyya (II)

LABARAI MASU NASABA

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.