ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Ta’addanci Ya Samu Gindin Zama A Arewa – Tsofaffin Janarori

by Sani Anwar and Sulaiman
5 months ago
Ta'addanci

Manyan tsoffin hafsoshin soji da kwararru a harkar tsaro da suka yi ritaya, sun bayyana dalilin da ya sa ake ci gaba da samun yawaitar sace-sacen mutane da ‘yan bindiga a Arewa, duk da kokarin da ake yi na ganin an shawo kan matsalar.

Sun danganta al’amarin ne da rashin tantance matsalar da kuma rashin tsaro a yankunan karkara da ake kai wadannan hare-hare.

  • Gobara Ta Sake Tashi A Kasuwar Singa A Kano
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ankarar Da Masu Kiwon Kaji Kan Ɓullar Murar Tsintsaye

Jihohin Katsina, Zamfara, Kaduna, Sakkwato da Neja, sun sha fama da hare-haren da ba su ji ba, ba su gani ba a ‘yan kwanakin nan.

ADVERTISEMENT

Haka zalika, a kwanakin baya, Jihar Kwara ta shiga tsaka mai wuya, inda wadannan ‘yan ta’adda suka shiga cikin al’ummarta, suka yi mummunar barna.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, a ranar 26 ga Nuwamban 2025, ya ayyana dokar ta-baci a dukkanin fadin wannan kasa, sannan ya umarci sojoji da ‘yansanda, da su dauki dubunnan karin jami’ai, domin magance munanan tashe-tashen hankula a fadin kasar.

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

Har ila yau, Tinubu ya umurci ‘yansanda da su dauki karin jami’ai 20,000, tare da bayar da izinin amfani da sansanonin masu yi wa kasa hidima a matsayin wuraren horaswa.

Kazalika, ya kuma bayar da umarnin janye jami’an ‘yansanda daga aikin gadi na manyan mutane (BIP), don sake tura su wuraren da ake fama da rikici, bayan sake horas da su.

Amma, fiye da wata biyu kenan bayan wadannan sanarwa, ba a ga wani gagarumin sauyi a tsakanin al’ummomin da ke fama da wadannan matsaloli ba.

Manjo Janar Chris Olukolade mai ritaya, wanda tsohon mai magana da yawun rundunar tsaro ne, ya alakanta matsalar ta’addancin kan rashin kula da iyakoki yadda ya kamata da kuma nuna banbance-bancen addini da siyasa.

Ya ce, wadannan su ne manyan tushen da suka sa ake ci gaba da aikata laifuka a yankin.

Har ila yau, ya kara da cewa; “Wani batu kuma shi ne, matsalar ra’ayin addini da siyasa da son zuciya, na matukar taimakawa wajen ta’azzarar wadannan laifukan.”

Ya ci gaba da cewa, sakacin da mutane suka yi da kuma rashin jajircewar gwamnati, na daya daga cikin abubuwan da suka kara taimakawa wajen tabarbarewar lamarin.

“Sakacin da aka samu daga wurin wasu al’ummomin, musamman ta fuskar zamantakewa da tattalin arzikin jama’a da kuma rashin isassun matakai, don kawo karshen rikicin, sun taimaka kwarai da gaske,” in ji shi.

Birgediya Janar Sani Usman mai ritaya, ya danganta rashin iya magance matsalar rashin tsaron da matsalar rashin hadin kai wajen daukar matakan da suka dace da kuma rashin fahimtar rikicin shi kansa.

Ya zargi “rashin kwararrun masu bincike da gudanar mulki” da bazuwar wannan rashin tsaro da ake fama da shi.

Manajan Darakta na ‘Beacon Security and Intelligence Ltd’, Dakta Kabir Adamu ya ce; wata biyu bayan sanarwar Shugaba Tinubu, babu wani abu da ya canza sosai, saboda har yanzu al’ummomin karkara na cikin matsalar rashin tsaro.

“Gwamnatin tarayya ta gaza wajen gudanar da harkokin tsaro, sannan majalisar tsaro ta kasa, ita ma tag a gaza a matsayin hukumar da ke kula da harkokin tsaron kasarmu, kazalika kuma, majalisar dokokin kasar ta gaza wajen gudanar da ayyukanta na tabbatar da bin doka da oda a bangaren tsaro,” in ji shi.

Haka nan, ya kuma zargi gwamnonin jihohi da rashin yin abin da ya dace, wajen tabbatar da tsaron ‘yan kasa.

“Gwamnoni, wadanda su ne shugabannin tsaro na jihohi daban-daban, wadanda suke karbar kudaden tsaro, suna kashewa amma babu wani abin a zo a gani da suke yi a jihohin nasu,” in ji shi.

Ta'addanci
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe
Ta'addanci
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
An Nuna Bidiyon Gabatarwar Shirye-Shiryen Bikin Bazara Na CMG A Sassan Afirka

An Nuna Bidiyon Gabatarwar Shirye-Shiryen Bikin Bazara Na CMG A Sassan Afirka

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.