Manyan tsoffin hafsoshin soji da kwararru a harkar tsaro da suka yi ritaya, sun bayyana dalilin da ya sa ake ci gaba da samun yawaitar sace-sacen mutane da ‘yan bindiga a Arewa, duk da kokarin da ake yi na ganin an shawo kan matsalar.
Sun danganta al’amarin ne da rashin tantance matsalar da kuma rashin tsaro a yankunan karkara da ake kai wadannan hare-hare.
- Gobara Ta Sake Tashi A Kasuwar Singa A Kano
- Gwamnatin Tarayya Ta Ankarar Da Masu Kiwon Kaji Kan Ɓullar Murar Tsintsaye
Jihohin Katsina, Zamfara, Kaduna, Sakkwato da Neja, sun sha fama da hare-haren da ba su ji ba, ba su gani ba a ‘yan kwanakin nan.
Haka zalika, a kwanakin baya, Jihar Kwara ta shiga tsaka mai wuya, inda wadannan ‘yan ta’adda suka shiga cikin al’ummarta, suka yi mummunar barna.
Shugaba Bola Ahmed Tinubu, a ranar 26 ga Nuwamban 2025, ya ayyana dokar ta-baci a dukkanin fadin wannan kasa, sannan ya umarci sojoji da ‘yansanda, da su dauki dubunnan karin jami’ai, domin magance munanan tashe-tashen hankula a fadin kasar.
Har ila yau, Tinubu ya umurci ‘yansanda da su dauki karin jami’ai 20,000, tare da bayar da izinin amfani da sansanonin masu yi wa kasa hidima a matsayin wuraren horaswa.
Kazalika, ya kuma bayar da umarnin janye jami’an ‘yansanda daga aikin gadi na manyan mutane (BIP), don sake tura su wuraren da ake fama da rikici, bayan sake horas da su.
Amma, fiye da wata biyu kenan bayan wadannan sanarwa, ba a ga wani gagarumin sauyi a tsakanin al’ummomin da ke fama da wadannan matsaloli ba.
Manjo Janar Chris Olukolade mai ritaya, wanda tsohon mai magana da yawun rundunar tsaro ne, ya alakanta matsalar ta’addancin kan rashin kula da iyakoki yadda ya kamata da kuma nuna banbance-bancen addini da siyasa.
Ya ce, wadannan su ne manyan tushen da suka sa ake ci gaba da aikata laifuka a yankin.
Har ila yau, ya kara da cewa; “Wani batu kuma shi ne, matsalar ra’ayin addini da siyasa da son zuciya, na matukar taimakawa wajen ta’azzarar wadannan laifukan.”
Ya ci gaba da cewa, sakacin da mutane suka yi da kuma rashin jajircewar gwamnati, na daya daga cikin abubuwan da suka kara taimakawa wajen tabarbarewar lamarin.
“Sakacin da aka samu daga wurin wasu al’ummomin, musamman ta fuskar zamantakewa da tattalin arzikin jama’a da kuma rashin isassun matakai, don kawo karshen rikicin, sun taimaka kwarai da gaske,” in ji shi.
Birgediya Janar Sani Usman mai ritaya, ya danganta rashin iya magance matsalar rashin tsaron da matsalar rashin hadin kai wajen daukar matakan da suka dace da kuma rashin fahimtar rikicin shi kansa.
Ya zargi “rashin kwararrun masu bincike da gudanar mulki” da bazuwar wannan rashin tsaro da ake fama da shi.
Manajan Darakta na ‘Beacon Security and Intelligence Ltd’, Dakta Kabir Adamu ya ce; wata biyu bayan sanarwar Shugaba Tinubu, babu wani abu da ya canza sosai, saboda har yanzu al’ummomin karkara na cikin matsalar rashin tsaro.
“Gwamnatin tarayya ta gaza wajen gudanar da harkokin tsaro, sannan majalisar tsaro ta kasa, ita ma tag a gaza a matsayin hukumar da ke kula da harkokin tsaron kasarmu, kazalika kuma, majalisar dokokin kasar ta gaza wajen gudanar da ayyukanta na tabbatar da bin doka da oda a bangaren tsaro,” in ji shi.
Haka nan, ya kuma zargi gwamnonin jihohi da rashin yin abin da ya dace, wajen tabbatar da tsaron ‘yan kasa.
“Gwamnoni, wadanda su ne shugabannin tsaro na jihohi daban-daban, wadanda suke karbar kudaden tsaro, suna kashewa amma babu wani abin a zo a gani da suke yi a jihohin nasu,” in ji shi.















Discussion about this post