ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Ta’addanci Ya Samu Gindin Zama A Arewa – Tsofaffin Janarori

by Sani Anwar and Sulaiman
4 months ago
Ta'addanci

Manyan tsoffin hafsoshin soji da kwararru a harkar tsaro da suka yi ritaya, sun bayyana dalilin da ya sa ake ci gaba da samun yawaitar sace-sacen mutane da ‘yan bindiga a Arewa, duk da kokarin da ake yi na ganin an shawo kan matsalar.

Sun danganta al’amarin ne da rashin tantance matsalar da kuma rashin tsaro a yankunan karkara da ake kai wadannan hare-hare.

  • Gobara Ta Sake Tashi A Kasuwar Singa A Kano
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ankarar Da Masu Kiwon Kaji Kan Ɓullar Murar Tsintsaye

Jihohin Katsina, Zamfara, Kaduna, Sakkwato da Neja, sun sha fama da hare-haren da ba su ji ba, ba su gani ba a ‘yan kwanakin nan.

ADVERTISEMENT

Haka zalika, a kwanakin baya, Jihar Kwara ta shiga tsaka mai wuya, inda wadannan ‘yan ta’adda suka shiga cikin al’ummarta, suka yi mummunar barna.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, a ranar 26 ga Nuwamban 2025, ya ayyana dokar ta-baci a dukkanin fadin wannan kasa, sannan ya umarci sojoji da ‘yansanda, da su dauki dubunnan karin jami’ai, domin magance munanan tashe-tashen hankula a fadin kasar.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

Har ila yau, Tinubu ya umurci ‘yansanda da su dauki karin jami’ai 20,000, tare da bayar da izinin amfani da sansanonin masu yi wa kasa hidima a matsayin wuraren horaswa.

Kazalika, ya kuma bayar da umarnin janye jami’an ‘yansanda daga aikin gadi na manyan mutane (BIP), don sake tura su wuraren da ake fama da rikici, bayan sake horas da su.

Amma, fiye da wata biyu kenan bayan wadannan sanarwa, ba a ga wani gagarumin sauyi a tsakanin al’ummomin da ke fama da wadannan matsaloli ba.

Manjo Janar Chris Olukolade mai ritaya, wanda tsohon mai magana da yawun rundunar tsaro ne, ya alakanta matsalar ta’addancin kan rashin kula da iyakoki yadda ya kamata da kuma nuna banbance-bancen addini da siyasa.

Ya ce, wadannan su ne manyan tushen da suka sa ake ci gaba da aikata laifuka a yankin.

Har ila yau, ya kara da cewa; “Wani batu kuma shi ne, matsalar ra’ayin addini da siyasa da son zuciya, na matukar taimakawa wajen ta’azzarar wadannan laifukan.”

Ya ci gaba da cewa, sakacin da mutane suka yi da kuma rashin jajircewar gwamnati, na daya daga cikin abubuwan da suka kara taimakawa wajen tabarbarewar lamarin.

“Sakacin da aka samu daga wurin wasu al’ummomin, musamman ta fuskar zamantakewa da tattalin arzikin jama’a da kuma rashin isassun matakai, don kawo karshen rikicin, sun taimaka kwarai da gaske,” in ji shi.

Birgediya Janar Sani Usman mai ritaya, ya danganta rashin iya magance matsalar rashin tsaron da matsalar rashin hadin kai wajen daukar matakan da suka dace da kuma rashin fahimtar rikicin shi kansa.

Ya zargi “rashin kwararrun masu bincike da gudanar mulki” da bazuwar wannan rashin tsaro da ake fama da shi.

Manajan Darakta na ‘Beacon Security and Intelligence Ltd’, Dakta Kabir Adamu ya ce; wata biyu bayan sanarwar Shugaba Tinubu, babu wani abu da ya canza sosai, saboda har yanzu al’ummomin karkara na cikin matsalar rashin tsaro.

“Gwamnatin tarayya ta gaza wajen gudanar da harkokin tsaro, sannan majalisar tsaro ta kasa, ita ma tag a gaza a matsayin hukumar da ke kula da harkokin tsaron kasarmu, kazalika kuma, majalisar dokokin kasar ta gaza wajen gudanar da ayyukanta na tabbatar da bin doka da oda a bangaren tsaro,” in ji shi.

Haka nan, ya kuma zargi gwamnonin jihohi da rashin yin abin da ya dace, wajen tabbatar da tsaron ‘yan kasa.

“Gwamnoni, wadanda su ne shugabannin tsaro na jihohi daban-daban, wadanda suke karbar kudaden tsaro, suna kashewa amma babu wani abin a zo a gani da suke yi a jihohin nasu,” in ji shi.

Ta'addanci
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Ta'addanci
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
  • Sulaiman
    Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
An Nuna Bidiyon Gabatarwar Shirye-Shiryen Bikin Bazara Na CMG A Sassan Afirka

An Nuna Bidiyon Gabatarwar Shirye-Shiryen Bikin Bazara Na CMG A Sassan Afirka

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.