ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Ta’addanci Ya Samu Gindin Zama A Arewa – Tsofaffin Janarori

by Sani Anwar and Sulaiman
4 months ago
Ta'addanci

Manyan tsoffin hafsoshin soji da kwararru a harkar tsaro da suka yi ritaya, sun bayyana dalilin da ya sa ake ci gaba da samun yawaitar sace-sacen mutane da ‘yan bindiga a Arewa, duk da kokarin da ake yi na ganin an shawo kan matsalar.

Sun danganta al’amarin ne da rashin tantance matsalar da kuma rashin tsaro a yankunan karkara da ake kai wadannan hare-hare.

  • Gobara Ta Sake Tashi A Kasuwar Singa A Kano
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ankarar Da Masu Kiwon Kaji Kan Ɓullar Murar Tsintsaye

Jihohin Katsina, Zamfara, Kaduna, Sakkwato da Neja, sun sha fama da hare-haren da ba su ji ba, ba su gani ba a ‘yan kwanakin nan.

ADVERTISEMENT

Haka zalika, a kwanakin baya, Jihar Kwara ta shiga tsaka mai wuya, inda wadannan ‘yan ta’adda suka shiga cikin al’ummarta, suka yi mummunar barna.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, a ranar 26 ga Nuwamban 2025, ya ayyana dokar ta-baci a dukkanin fadin wannan kasa, sannan ya umarci sojoji da ‘yansanda, da su dauki dubunnan karin jami’ai, domin magance munanan tashe-tashen hankula a fadin kasar.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

Har ila yau, Tinubu ya umurci ‘yansanda da su dauki karin jami’ai 20,000, tare da bayar da izinin amfani da sansanonin masu yi wa kasa hidima a matsayin wuraren horaswa.

Kazalika, ya kuma bayar da umarnin janye jami’an ‘yansanda daga aikin gadi na manyan mutane (BIP), don sake tura su wuraren da ake fama da rikici, bayan sake horas da su.

Amma, fiye da wata biyu kenan bayan wadannan sanarwa, ba a ga wani gagarumin sauyi a tsakanin al’ummomin da ke fama da wadannan matsaloli ba.

Manjo Janar Chris Olukolade mai ritaya, wanda tsohon mai magana da yawun rundunar tsaro ne, ya alakanta matsalar ta’addancin kan rashin kula da iyakoki yadda ya kamata da kuma nuna banbance-bancen addini da siyasa.

Ya ce, wadannan su ne manyan tushen da suka sa ake ci gaba da aikata laifuka a yankin.

Har ila yau, ya kara da cewa; “Wani batu kuma shi ne, matsalar ra’ayin addini da siyasa da son zuciya, na matukar taimakawa wajen ta’azzarar wadannan laifukan.”

Ya ci gaba da cewa, sakacin da mutane suka yi da kuma rashin jajircewar gwamnati, na daya daga cikin abubuwan da suka kara taimakawa wajen tabarbarewar lamarin.

“Sakacin da aka samu daga wurin wasu al’ummomin, musamman ta fuskar zamantakewa da tattalin arzikin jama’a da kuma rashin isassun matakai, don kawo karshen rikicin, sun taimaka kwarai da gaske,” in ji shi.

Birgediya Janar Sani Usman mai ritaya, ya danganta rashin iya magance matsalar rashin tsaron da matsalar rashin hadin kai wajen daukar matakan da suka dace da kuma rashin fahimtar rikicin shi kansa.

Ya zargi “rashin kwararrun masu bincike da gudanar mulki” da bazuwar wannan rashin tsaro da ake fama da shi.

Manajan Darakta na ‘Beacon Security and Intelligence Ltd’, Dakta Kabir Adamu ya ce; wata biyu bayan sanarwar Shugaba Tinubu, babu wani abu da ya canza sosai, saboda har yanzu al’ummomin karkara na cikin matsalar rashin tsaro.

“Gwamnatin tarayya ta gaza wajen gudanar da harkokin tsaro, sannan majalisar tsaro ta kasa, ita ma tag a gaza a matsayin hukumar da ke kula da harkokin tsaron kasarmu, kazalika kuma, majalisar dokokin kasar ta gaza wajen gudanar da ayyukanta na tabbatar da bin doka da oda a bangaren tsaro,” in ji shi.

Haka nan, ya kuma zargi gwamnonin jihohi da rashin yin abin da ya dace, wajen tabbatar da tsaron ‘yan kasa.

“Gwamnoni, wadanda su ne shugabannin tsaro na jihohi daban-daban, wadanda suke karbar kudaden tsaro, suna kashewa amma babu wani abin a zo a gani da suke yi a jihohin nasu,” in ji shi.

Ta'addanci
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Ta'addanci
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
An Nuna Bidiyon Gabatarwar Shirye-Shiryen Bikin Bazara Na CMG A Sassan Afirka

An Nuna Bidiyon Gabatarwar Shirye-Shiryen Bikin Bazara Na CMG A Sassan Afirka

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.