ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

AFCON 2025: CAF Ta Ci Tarar Algeria, Ta Dakatar Da Ƴan Wasanta

by Abubakar Sulaiman
6 months ago
AFCON

Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Afrika (CAF) ta ɗauki matakai masu tsauri kan ƙasar Algeria da wasu ƴan wasanta bayan rashin ɗa’a da suka nuna a lokacin da kuma bayan wasan daf da na kusa da na ƙarshe na Gasar AFCON 2025 da suka fafata da Nijeriya.

A cikin wata sanarwa da CAF ta fitar a ranar Laraba, ta ce Kwamitin Ladabtarwarta ya zauna domin duba abubuwan da suka faru a wasan da aka buga ranar 10 ga Janairu, 2026, inda ya yanke hukunci da dama.

Daga ciki sun haɗa da Mai tsaron ragar Algeria, Luca Zidane, an dakatar da shi daga buga wasanni biyu na CAF saboda rashin ɗa’a, yayin da mai tsaron baya Rafik Belghali ya samu dakatarwa na wasanni huɗu bisa zargin nuna halin tsokana da tsoratarwa ga alƙalin wasa a ƙarshen wasan, amma wasanni biyu daga ciki an dakatar da aiwatar da su na tsawon shekara guda a matsayin gwaji.

ADVERTISEMENT
  • AFCON 2025: Lookman Da Osimhen Na Daga Cikin Zaratan Yan Wasa 11 Na Bana
  • Gwmantin Kaduna Ta Tabbatar Da Sace Masu Ibada 177 A Kajuru

Haka kuma, CAF ta ci hukumar Ƙwallon Ƙafar Algeria (FAF) tarar kuɗi har dala 100,000 bisa halayen ƴan wasa, jami’ai da magoya baya. Tarar ta haɗa da dala 5,000 saboda katunan gargaɗi biyar da ƙungiyar ta samu, da dala 25,000 saboda halayen da suka ɓata martabar wasan a ƙarshen wasa, da dala 5,000 saboda amfani da hayaƙi daga magoya baya, da dala 5,000 saboda jefa abubuwa cikin fili, da dala 10,000 saboda gazawa wajen bin matakan tsaro, da kuma dala 50,000 saboda nuna halaye na cin zarafi ga jami’an wasa.

CAF ta bayyana cewa ba a ɗauki wani mataki kan ƙungiyar Nijeriya ba dangane da lamarin. Rikicin ya ɓarke ne bayan an busa tashi a ƙarshe, yayin da Super Eagles ta tsallake zuwa gaba a tsakiyar zanga-zangar ƴan Algeria da magoya bayansu kan ƙwallayen da ake takaddama a kansu, musamman zargin rashin ba su bugun fanareti.

LABARAI MASU NASABA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

Bidiyoyi da suka yaɗu a kafafen sada zumunta sun nuna ƴan Algeria na tunkarar alƙalai da yin arangama, yayin da magoya baya ke jefa abubuwa da karya shingayen tsaro. Tarayyar Ƙwallon Ƙafar Algeria ta ce za ta ɗaukaka ƙara, tana kallon hukuncin a matsayin mai tsauri tare da neman a sake duba aikin alkalanci.

AFCON
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark
  • Abubakar Sulaiman
    Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato
  • Abubakar Sulaiman
    FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

MASU ALAKA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
Wasanni

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
Wasanni

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Wasanni

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

July 11, 2026
Next Post
“Ba Neman Kuɗi Nake Yi Ba, Na Shiga Siyasa Ne Don Ceto Al’umma” – Tsohon Shugaban DSS

“Ba Neman Kuɗi Nake Yi Ba, Na Shiga Siyasa Ne Don Ceto Al'umma” - Tsohon Shugaban DSS

LABARAI MASU NASABA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.