ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

AFCON 2025: CAF Ta Ci Tarar Algeria, Ta Dakatar Da Ƴan Wasanta

by Abubakar Sulaiman
5 months ago
AFCON

Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Afrika (CAF) ta ɗauki matakai masu tsauri kan ƙasar Algeria da wasu ƴan wasanta bayan rashin ɗa’a da suka nuna a lokacin da kuma bayan wasan daf da na kusa da na ƙarshe na Gasar AFCON 2025 da suka fafata da Nijeriya.

A cikin wata sanarwa da CAF ta fitar a ranar Laraba, ta ce Kwamitin Ladabtarwarta ya zauna domin duba abubuwan da suka faru a wasan da aka buga ranar 10 ga Janairu, 2026, inda ya yanke hukunci da dama.

Daga ciki sun haɗa da Mai tsaron ragar Algeria, Luca Zidane, an dakatar da shi daga buga wasanni biyu na CAF saboda rashin ɗa’a, yayin da mai tsaron baya Rafik Belghali ya samu dakatarwa na wasanni huɗu bisa zargin nuna halin tsokana da tsoratarwa ga alƙalin wasa a ƙarshen wasan, amma wasanni biyu daga ciki an dakatar da aiwatar da su na tsawon shekara guda a matsayin gwaji.

ADVERTISEMENT
  • AFCON 2025: Lookman Da Osimhen Na Daga Cikin Zaratan Yan Wasa 11 Na Bana
  • Gwmantin Kaduna Ta Tabbatar Da Sace Masu Ibada 177 A Kajuru

Haka kuma, CAF ta ci hukumar Ƙwallon Ƙafar Algeria (FAF) tarar kuɗi har dala 100,000 bisa halayen ƴan wasa, jami’ai da magoya baya. Tarar ta haɗa da dala 5,000 saboda katunan gargaɗi biyar da ƙungiyar ta samu, da dala 25,000 saboda halayen da suka ɓata martabar wasan a ƙarshen wasa, da dala 5,000 saboda amfani da hayaƙi daga magoya baya, da dala 5,000 saboda jefa abubuwa cikin fili, da dala 10,000 saboda gazawa wajen bin matakan tsaro, da kuma dala 50,000 saboda nuna halaye na cin zarafi ga jami’an wasa.

CAF ta bayyana cewa ba a ɗauki wani mataki kan ƙungiyar Nijeriya ba dangane da lamarin. Rikicin ya ɓarke ne bayan an busa tashi a ƙarshe, yayin da Super Eagles ta tsallake zuwa gaba a tsakiyar zanga-zangar ƴan Algeria da magoya bayansu kan ƙwallayen da ake takaddama a kansu, musamman zargin rashin ba su bugun fanareti.

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

Bidiyoyi da suka yaɗu a kafafen sada zumunta sun nuna ƴan Algeria na tunkarar alƙalai da yin arangama, yayin da magoya baya ke jefa abubuwa da karya shingayen tsaro. Tarayyar Ƙwallon Ƙafar Algeria ta ce za ta ɗaukaka ƙara, tana kallon hukuncin a matsayin mai tsauri tare da neman a sake duba aikin alkalanci.

AFCON
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Sowore A Gidan Yarin Kuje
  • Abubakar Sulaiman
    Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

MASU ALAKA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino
Wasanni

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
Wasanni

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

June 22, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
Wasanni

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
Next Post
“Ba Neman Kuɗi Nake Yi Ba, Na Shiga Siyasa Ne Don Ceto Al’umma” – Tsohon Shugaban DSS

“Ba Neman Kuɗi Nake Yi Ba, Na Shiga Siyasa Ne Don Ceto Al'umma” - Tsohon Shugaban DSS

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.