ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

AFCON 2025: CAF Ta Ci Tarar Algeria, Ta Dakatar Da Ƴan Wasanta

by Abubakar Sulaiman
8 months ago
AFCON

Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Afrika (CAF) ta ɗauki matakai masu tsauri kan ƙasar Algeria da wasu ƴan wasanta bayan rashin ɗa’a da suka nuna a lokacin da kuma bayan wasan daf da na kusa da na ƙarshe na Gasar AFCON 2025 da suka fafata da Nijeriya.

A cikin wata sanarwa da CAF ta fitar a ranar Laraba, ta ce Kwamitin Ladabtarwarta ya zauna domin duba abubuwan da suka faru a wasan da aka buga ranar 10 ga Janairu, 2026, inda ya yanke hukunci da dama.

Daga ciki sun haɗa da Mai tsaron ragar Algeria, Luca Zidane, an dakatar da shi daga buga wasanni biyu na CAF saboda rashin ɗa’a, yayin da mai tsaron baya Rafik Belghali ya samu dakatarwa na wasanni huɗu bisa zargin nuna halin tsokana da tsoratarwa ga alƙalin wasa a ƙarshen wasan, amma wasanni biyu daga ciki an dakatar da aiwatar da su na tsawon shekara guda a matsayin gwaji.

ADVERTISEMENT
  • AFCON 2025: Lookman Da Osimhen Na Daga Cikin Zaratan Yan Wasa 11 Na Bana
  • Gwmantin Kaduna Ta Tabbatar Da Sace Masu Ibada 177 A Kajuru

Haka kuma, CAF ta ci hukumar Ƙwallon Ƙafar Algeria (FAF) tarar kuɗi har dala 100,000 bisa halayen ƴan wasa, jami’ai da magoya baya. Tarar ta haɗa da dala 5,000 saboda katunan gargaɗi biyar da ƙungiyar ta samu, da dala 25,000 saboda halayen da suka ɓata martabar wasan a ƙarshen wasa, da dala 5,000 saboda amfani da hayaƙi daga magoya baya, da dala 5,000 saboda jefa abubuwa cikin fili, da dala 10,000 saboda gazawa wajen bin matakan tsaro, da kuma dala 50,000 saboda nuna halaye na cin zarafi ga jami’an wasa.

CAF ta bayyana cewa ba a ɗauki wani mataki kan ƙungiyar Nijeriya ba dangane da lamarin. Rikicin ya ɓarke ne bayan an busa tashi a ƙarshe, yayin da Super Eagles ta tsallake zuwa gaba a tsakiyar zanga-zangar ƴan Algeria da magoya bayansu kan ƙwallayen da ake takaddama a kansu, musamman zargin rashin ba su bugun fanareti.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

Bidiyoyi da suka yaɗu a kafafen sada zumunta sun nuna ƴan Algeria na tunkarar alƙalai da yin arangama, yayin da magoya baya ke jefa abubuwa da karya shingayen tsaro. Tarayyar Ƙwallon Ƙafar Algeria ta ce za ta ɗaukaka ƙara, tana kallon hukuncin a matsayin mai tsauri tare da neman a sake duba aikin alkalanci.

AFCON
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Sokoto, Sun Kashe Mutane 7, Sun Yi Garkuwa Da 12

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
Wasanni

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

September 8, 2026
Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
Wasanni

Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain

September 7, 2026
Next Post
“Ba Neman Kuɗi Nake Yi Ba, Na Shiga Siyasa Ne Don Ceto Al’umma” – Tsohon Shugaban DSS

“Ba Neman Kuɗi Nake Yi Ba, Na Shiga Siyasa Ne Don Ceto Al'umma” - Tsohon Shugaban DSS

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.