ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Wani  Hedimasta Bisa Laifin Sayar Da Kayayyakin Makaranta A Kano

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Makaranta

Hukumar Karbar Korafe-Korafen Jama’a Da Yaki Da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano ta kama sakataren ilimi, shugaban makarantar, da wasu mutane uku bisa zargin tarwatsawa tare da sayar da kayayyaki da suka shafi karafa na makaranta ba bisa ka’ida ba a makarantar firamare da ke Karamar Hukumar Kumbotso. Wadanda ake zargin, da aka kama, an kama su ne a harabar makarantar.

Babban mai ba da rahoto na musamman ga Gwamnan Jihar Kano kan yaki da cin hanci da rashawa, Malam Sani Umar Sani, wanda ya tabbatar wa da wakilinmu kamen a ranar Lahadin da ta gabata, ya ce wasu mazauna unguwar da suke motsa jiki da sanyin safiyar ranar Asabar, sun ji waani motsi da hayaniya a tashar Gaidar Makada Special Primary School, Karamar Hukumar Kumbotso.

  • Mutum 2 Sun Rasu Yayin Da Bene Ya Rushe Da Su A Kano 
  • Zabukan Cikin Gida Na Jam’iyyar PDP: Ya Kamata A Kwance Rigiza!

A binciken da aka yi na kurkusa, ya ce sun gano cewa an wargaza kayan makarantar da karafa da aka hada aka kwashe.

ADVERTISEMENT

“Daya daga cikin mazauna unguwar da ke makotaka da makarantar ya ce da sanyin safiyar ranar Asabar ne ya ga wani mutum tare da wasu yara maza suka nufi ajujuwan makarantar amma jami’in tsaro ya kama su, bayan wani dan bayani aka ba shi damar shiga ajujuwan,” Sani ya bayyana wa manema labarai.

“Bayan haka, magidancin ya ce ya jiyo hayaniya sosai daga ajujuwan, wanda hakan ta sa ya yaynke shawarar duba da kyau, inda a gano cewa ba kawai tarwatsa kayan makarantar ake bay i ba har ma da hada kan wasu karafa domin yin awon gaba da su.

LABARAI MASU NASABA

An Tantance Masu Neman Aikin Koyarwa 500 A Jigawa

JAMB Ta Ƙara Wa’adin Amincewar Guraben Karatu Zuwa 30 Satumba

“Daga baya ya sanar da Shugaban Kwamitin Gudanarwa na Makaranta, Malam AbdulGafar Sanusi Garba, wanda ya ce bai san da wannan aikin ba, yayin da Shugaban Kungiyar Malamai ta Iyaye, Malam Alkassim Muhammad, shi ma aka sanar da shi.

A cewarsu, ba su da wata masaniya kan hakan, domin shugaban makarantar ya kore su kafin cikar wa’adinsu.

Sun ce an sanar da sakataren ilimi na karamar hukumar cewa shugaban makarantar ya sauke su ta wani bangare daban bayan kuma su al’umma ce ta nada su.

“Da muka tuntubi Sakataren shi, ya yi alkawarin duba lamarin amma har yanzu ba mu ji komai daga gare shi ba.

“Ci gaban da muka lura da shi a safiyar yau, mun tambaye su dalilin da ya sa suke wargaza kujerun makarantar da sauran kayayyaki, sai suka ce za a sayar da kayayyakin ne ga mutanen da suke shirya saya bisa ga umarnin hukumar makarantar.

“Ba tare da bata lokaci ba muka dauki bidiyon abubuwan kuma muka sanar da hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta jihar.”

Wata majiya da ke kusa da hukumar da ta nemi a sakaya sunanta, ta ce daga cikin wadanda aka kama har da daya daga cikin ‘yan kasuwar, wanda ya sayi karafa da sandunan karfe daga cikin kayayyakin.

Bugu da kari, PUNCH Metro ta samu labarin cewa wadanda ake zargin sun sayar da kayayyakin da aka lalatar da suka haura Naira miliyan 2 akan Naira 250,000.

Har ila yau, an ruwaito cewa Hukumar Yaki da cin hanci da rashawa ta kaddamar da bincike kan lamarin, domin wadanda aka kama suna hannun ta.

Har ila yau, wata majiya mai tushe a hukumar ta shaida wa wakilinmu cewa, hakan na iya zama dalilin wargaza kayayyakin a mafi yawan makarantun firamare da ke jihar ba bisa ka’ida ba.

Majiyar ta ci gaba da cewa tuni hukumar ta fara aikin samar da manhajoji da za su rika tattara kayan aiki a makarantun da ke fadin jihar tare da sanar da ita idan wani daga cikinsu ya

Makaranta
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Makaranta
Ilimi

An Tantance Masu Neman Aikin Koyarwa 500 A Jigawa

August 31, 2026
Makaranta
Ilimi

JAMB Ta Ƙara Wa’adin Amincewar Guraben Karatu Zuwa 30 Satumba

August 29, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Ilimi

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

July 11, 2026
Next Post
Sabon Matakin FOCAC Na Jagorantar Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Wajen Zamanintar Da Al’umomminsu

Sabon Matakin FOCAC Na Jagorantar Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Wajen Zamanintar Da Al’umomminsu

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.