ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Askarawan Zamfara Da Aka Kashe Sun Nuna Sadaukarwa, Za Mu Kula Da Iyalansu – Gwamna Dauda

-Ya Ce Ba Za Su Sarara Da Fatattakar 'Yan Bindiga A Jihar Ba

by Leadership Hausa
2 years ago
zamfara

Gwamna Dauda Lawal ya yi alƙawarin gwamnatinsa za ta bayar da cikakkiyar kulawa ga iyalan jami’an Askarawan Zamfara da aka kashe a wani kwanton ɓaunar da aka yi masu.

Gwamnan ya yi wannan alƙawarin ne a fadar ‘Yan Doton Tsafe lokacin da ya kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan jami’an Askarawan Zamfara da ‘yan bindiga suka yi wa kwanton ɓauna a cikin makon da ya gabata.

Yayin jajanta wa masarautar da kuma Iyalan waɗanda aka kashen, Gwamna Lawal ya nuna cewa wannan sadaukarwa da jami’an suka yi, ba za ta tafi a banza ba.

ADVERTISEMENT
  • Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

A cikin wata sanarwa da ya fitar yau a Gusau, Mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya ambato Gwamna Lawal yana cewa: “Na zo nan yau ne domin in miƙa ta’aziyyata ga masarauta, iyalai da al’ummar Tsafe bisa kisan da aka yi wa gwarazan mu, a wani kwanton ɓauna da aka yi masu.

zamfara

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

“Wannan wani bala’i ne wanda muka ji raɗaɗin sa matuƙa. Lallai mun shaida wannan tsayin-daka na waɗannan dakaru don kare rayukan al’ummar su.

“Ina jin wannan baƙin labari, sai na turo da wata ƙaƙƙarfar tawaga ta gwamnati, ƙarshin jagorancin Mataimakin Gwamna domin su zo su miƙa ta’aziyya ga masarauta da iyalan waɗanda abin ya shafa.

zamfara

“Ina tabbatar maku da cewa irin waɗannan abubuwan, ba za su dakatar da mu daga farmakin da muke kai wa ‘yan bindiga ba. Muna yin duk abin da ya wajaba wajen kawo ƙarshen ‘yan bindiga a jihar Zamfara.

“Gwamnatin jihar Zamfara za ta ɗauki duk ɗawainiyar iyalan waɗannan Asakarawan. Ina yin wannan alƙawari ne a nan, kuma za mu tabbatar mun cika shi.

Nan take kuma Gwamnan ya bayyana bayar da tallafin kuɗaɗe da kayan abinci ga iyalan mamatan.

A jawabin da ya gabatar, Sarkin Tsafe, Alhaji Muhammadu Bawa, ya nuna godiyar sa ga Gwamna Lawal, da kuma jijina masa bisa irin namijin ƙoƙarin da ya ke yi wajen samar da tsaro da jin daɗin al’umma.

zamfara
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi
Tsaro

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

June 19, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Manyan Labarai

Mata Ta Hallaka Mijinta Da Wuƙa Watanni Biyu Bayan Aure A Kano

June 17, 2026
Next Post
Yadda Muka Sanya Tinubu Ya Soke Kwangilar Aikin Hanyar Kankara Zuwa Katsina inji Ibrahim Masari 

Yadda Muka Sanya Tinubu Ya Soke Kwangilar Aikin Hanyar Kankara Zuwa Katsina inji Ibrahim Masari 

LABARAI MASU NASABA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.