Tsarin Ruhin Jam’iyyar Kwaminis Ta Sin Da Mambobinta Suke Bunkasawa Da Tantance Shi Tsawon Shekaru Dari
Shekaru 90 da suka gabata, wasu matasa sanye da takalman ciyawa suka haye tsaunuka masu dusar kankara da ratsa filin...
Shekaru 90 da suka gabata, wasu matasa sanye da takalman ciyawa suka haye tsaunuka masu dusar kankara da ratsa filin...
A yau Lahadi ne kasar Sin ta yi nasarar harba sabon rukunin taurarin dan Adam daga cibiyar harba kumbuna na...
Kakakin Ofishin jakadancin Sin dake kasar Japan, ya soki lamirin ziyarar da wasu manyan jami’an gwamnatin kasar Japan suka kai haikalin Yasukuni, matakin da ya ce ya illata nasarorin da aka cimma bayan yakin duniya na biyu, da odar kasa da kasa da aka cimma bayan yakin. Da yake amsa tambayar manema labarai dangane da batun a jiya Asabar, kakakin ya ce, ziyara da karrama haikalin Yasukuni, makwancin manyan kusoshin kasar da suka aikata munanan laifukan yaki yayin yakin duniya na biyu, wanda firaministanr kasar Sanae Takaichi, da wasu ministocin kasar, da manyan ‘yan siyasar Japan suka gudanar, abu ne da Sin ke matukar adawa da shi, kuma ta yi Allah wadai tare da gabatar da korafi mai karfi, da nuna rashin jin dadi kan hakan ga bangaren Japan. Kakakin ya kara da cewa, Sin na kira ga bangaren Japan da ya yi matukar karatun ta nutsu dangane da laifukan da ya aikata a tarihi, ya yi koyi daga abubuwan da suka gabata, ya martaba alkawuran neman ci gaba ta hanyar lumana, kana ya aiwatar da matakai na hakika don kaucewa amfani da karfin tuwo, da dakatar da mummunan yanayin sake farfado da rundunar soji, da kaucewa sake sanya kasar a matsayi na abar tuhuma a tarihi. (Saminu Alhassan)
Yayin da ake gudanar da babban taro kan ilimin ginshikin kimiyya na duniya wato ICBS na shekarar 2026 a birnin...
A gobe Lahadi, za a wallafa wata makala ta shugaba Xi Jinping, babban sakataren kwamitin tsakiya na Jam'iyyar Kwaminis ta...
Yau Asabar 15 ga watan nan ne ake cika shekaru 81 da mika wuyar da kasar Japan ta yi ba...
Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ya amsa tambayar da aka yi masa a yau Asabar 15...
A yau Asabar, kasar Sin ta dauki wani muhimmin mataki na tabbatar da zamanantarwa mara gurbata muhalli, yayin da dokarta...
Yau ranar 15 ga watan Agusta ita ce ranar kare muhalli ta kasar Sin karo na 4, haka kuma ita ce ranar da aka fara aiwatar da "Kundin Dokokin Kare Muhalli na kasar Sin" a hukumance. A daidai wannan lokaci, bari mu duba ci gaban da Sin ta samu a wannan fanni. Bisa alkaluman da aka samar, fadin dazuzzuka ya kai kashi 25% na filayen kasar, kana yawan bishiyoyi da itatuwa da aka dasa a yankunan arewa maso yammacin kasar da arewacinta da kuma arewa maso gabashinta domin inganta muhalli ya kai kashi 40.76%. Fadin kasar da ke fama da kwararowar hamada ya takaita daga kara fadi da eka dubu 343.333 a ko wace shekara zuwa raguwa da eka dubu 666.667 a ko wace shekara. Sin ta zama kasar da ta fi saurin karuwar dazuzzuka a duniya. A yayin da kasar Sin ke samun ci gaban inganta muhallinta, hadin gwiwar da ke tsakaninta da kasashen Afirka ta wannan fanni ma tana bunkasa yadda ya kamata. A watan Yuni na 2026, a taron koli na dandalin tattaunawa kan yanayin muhalli na duniya, an gudanar da wani taron na musamman mai taken "Koyi da kwarewar Sin don inganta yanayin muhalli a gabashin Afirka", wanda ya jawo hankulan jami'ai da masana daga kasashen Afirka da yawa da kungiyoyin kasa da kasa, inda suka tattauna batutuwan da suka shafi kyautata muhalli da samun ci gaba mai dorewa. Mahalarta taron sun kai ga cimma matsaya daya cewa, kwarewar Sin a fannin kare muhalli tana ba da muhimmiyar ma’ana ga matakin da Afirka ke dauka na karkata zuwa hanyar samun bunkasa ba tare da gurbata muhalli ba, kuma hadin gwiwar Sin da Afirka a wannan fanni na da makoma mai haske. A gefen hamada dake da nisan kimanin kilomita 70 daga Nouakchott, babban birnin Mauritania, Sin da Mauritania sun kafa "Lambun shan iska na gwaji mai amfani da fasahar Sin" mai fadin ekta 4 cikin hadin gwiwa. Masana daga cibiyar binciken muhalli da yanayin kasa ta yankin Xinjiang na Kwalejin nazarin kimiyya ta Sin sun kawo wa wannan yankin kwarewar shawo kan kwararar hamada. Ministan kare muhalli na Mauritania ya yi wa matakin da Sin ke dauka lakabin "juyin-juya-hali a bangaren kiyaye muhalli dake faruwa a yanzu." Tafkin Victoria da ke gabashin Afirka da tafkin Poyang na Sin suna fuskantar matsalolin muhalli kusan iri daya, wato kwan-gaba-kwan-bayan matsayin ruwa, da asarar mabambantan halittu da karuwar ayyukan dan Adam dake illata muhalli. Masanan Sin da Afirka suna musayar ra’ayoyi a bangarori daban-daban don magance wadannan matsaloli tare, ciki har da kyautata koguna daga dukkan fannoni da gudanar da aikin noma mai kiyaye muhalli da kayyade amfani da maganin kashe kwari da kuma amfani da makamashi mai tsabta kamar hasken rana. A Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo, kamfanin kasar Sin ya cimma gaggarumar nasara a bangaren samar da wutar lantarki bisa makamashi mai tsabta, injunan janareto masu samar da wutar lantarki da aka harhada a tashar samar da wutar lantarki ta Busanga na kasar sun kai karfin megawatt 240, kuma suna iya samar da wutar lantarki da yawanta ya kai KWH biliyan 1.32 mai amfani da makamashi mai tsabta a ko wace shekara, matakin da ya iya yin tsimin kwal tan dubu 447, tare da rage fitar da iskar "carbon dioxide" tan miliyan 1.1 a ko wace shekara. Sin da Afirka suna rubuta sabon tarihi wajen samun jituwa tsakanin mutum da muhalli. Ba shakka, hadin gwiwar Sin da Afirka a bangaren kare muhalli na da makoma mai haske.(Marubuciya: MINA)
Daga fim din "Schindler's List" zuwa "All Quiet on the Western Front", fina-finan da ke nuna adawa da yaki suna sosa zukatan jama’a. A...
© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.
© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.