NiMet Ta Yi Hasashen Ruwan Sama Da Tsawa Na Kwana Uku A Faɗin Nijeriya
Hukumar Kula da Yanayi ta Nijeriya (NiMet) ta yi hasashen yanayi daban-daban na tsawon kwanaki uku, ciki har da rana,...
Hukumar Kula da Yanayi ta Nijeriya (NiMet) ta yi hasashen yanayi daban-daban na tsawon kwanaki uku, ciki har da rana,...
Da yammacin yau Litinin 31 ga wata, shugaban kasar Sin Xi Jinping wanda ke halatar taron kolin kungiyar hadin gwiwa...
A daidai lokacin da ake gudanar da taron koli na kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai (SCO), daga yau 31 ga...
Shahararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa na duniya, Lionel Messi, ya sanar da yin ritaya daga buga wa ƙasar Argentina ƙwallon...
An ceto masu yi wa kasa hidima 10 (NYSC) da wasu ’yan bindiga suka yi garkuwa da su daga dajin...
Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Guo Jiakun, ya jagoranci wani taron manema labarai a yau Litinin...
Shugaban kasar Sin, Xi Jinping, ya isa birnin Bishkek a yau Lahadi domin halartar taron kolin Kungiyar Hadin Gwiwa ta Shanghai (SCO) na shekarar 2026, da kuma gudanar da ziyarar aiki a kasar Kyrgyzstan. Shugaban kasar Kyrgyzstan, Sadyr Japarov, da uwargidansa sun tarbi shugaba Xi Jinping da uwargidansa, Peng Liyuan, a filin jirgin saman kasa da kasa na Manas, a yau Lahadi. Shugaba Xi ya gabatar da sako a rubuce, a madadin gwamnati da al'ummar kasar Sin, inda ya mika kyakkyawar gaisuwa da fatan alheri ga shugaba Sadyr Japarov da al'ummar kasar Kyrgyzstan. Xi ya bayyana cewa, dangantakar abota tsakanin Sin da Kyrgyzstan tana da dogon tarihi da zamani mai alfanu, kuma tsaunukan Tianshan sun shaida musayar zumunta mai danko tsakanin al'ummomin biyu a tsawon dubban shekaru. Kazalika, tun bayan kulla huldar diflomasiyya shekaru 34 da suka gabata, dangantakar Sin da Kyrgyzstan ta tsallaka siradin sauye-sauyen siyasar duniya, tare da samun ci gaba mai inganci ba tare da tangarda ba, har ta kai matsayin hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare na matakin koli a sabon zamani. Shugaba Xi ya kara da cewa, a yayin wannan ziyara, zan yi cikakkiyar tattaunawa da shugaba Japarov kan dangantakar Sin da Kyrgyzstan, da hadin gwiwa a fannoni daban-daban, da kuma batutuwan kasa da kasa da na shiyya-shiyya kan muradun juna, domin tsara sabon shirin gina al'ummar Sin da Kyrgyzstan mai kyakkyawar makoma ta bai-daya. Ina fatan halartar taron kolin kungiyar SCO da za a gudanar a Bishkek, tare da yin aiki da dukkan bangarori don karfafa samun ci gaba mai dorewa ga Kungiyar Hadin Gwiwa ta Shanghai. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
A yayin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ke halartar taron koli na kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai wato SCO...
Ana ci gaba da aiwatar da shirin tallafin da Sin ta ware wa kasar Nepal, wanda ya hada da tallafin...
Da safiyar ranar 26 ga watan nan da muke ciki, an samu abkuwar mummunan ibtila’in zabtarewar kasa a bangaren kasar Nepal mai makwabtaka da kasar Sin, lamarin da ya janyo babbar hasarar rayuka gami da bacewar wasu mutane da dama a gundumar Gyirong ta birnin Xigaze na jihar Xizang mai cin gashin kanta ta kasar Sin, wato yankin kan iyakokin Sin da Nepal. A yau Lahadi kuma an yi wani taron manema labarai a Gyirong dangane da ibtila’in, inda aka bayyana cewa, bayan abkuwarsa, an dauki matakan shawo kansa ba tare da bata lokaci ba a Xizang, inda aka kafa babban sashin kula da ayyukan ba da agajin gaggawa gami da wani sashin kula da agajin gaggawa da ke can yankin da ibtila’in ya ritsa da shi. Ma’aikatar kudi, da ma’aikatar shawo kan al’amuran ba-zata ta kasar Sin, sun ware kudin Sin Yuan miliyan 120, kana, kwamitin samar da ci gaba da yin gyare-gyare a gida na kasar ya ware Yuan miliyan 100, a wani kokari na tallafa wa ayyukan ba da agaji da ceto da kuma farfado da yankin da ibtila’in ya shafa. Kawo yanzu, an riga an tura ma’aikata 2141 na bangarori daban-daban domin bayar da agajin gaggawa a wurin, ciki har da na rundunar ’yantar da jama’ar kasar Sin, da ’yan sanda masu dauke da makamai, da tawagar ’yan kwana-kwana masu kai dauki da sauransu, gami da motocin agaji guda 269, hade da na’urorin kai dauki 3922. Zuwa karfe 6 na yammacin ranar 29 ga watan muke ciki, yawan mutanen da suka rasa rayukansu sakamakon ibtila’in ya kai 16, yayin da wasu 546 suka bace. (Murtala Zhang)
© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.
© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.