Tsohon mataimakin gwamnan jihar Sokoto, Mukhtar Shagari, ya bayyana cewa gwamnan jihar, Siminalayi Fubara, da kansa ya yanke shawarar ficewa daga harkokin siyasar 2027 ba tare da wani matsin lamba daga waje ba.
Da yake magana a wata hira da gidan talabijin na Arise TV ranar Alhamis, Shagari ya ce Fubara shugaba ne kuma mai ilimi wanda yake da cikakken ‘yancin ɗaukar duk wata shawara ta siyasa da ta shafe shi, ciki har da janye kansa daga takara.
A cewarsa, gwamnan ya yanke shawarar ne bayan tattaunawa da shawarwari, kuma bai nuna cewa wani mutum ko wata ƙungiya ce ta tilasta masa hakan ba.
“Ya bayyana cewa shawarar ta biyo bayan tattaunawa kuma har yanzu yana nan daram cikin jam’iyyarsa. Haka kuma bai nuna cewa wani ya tilasta masa ko ya yi tasiri a kansa wajen yanke shawarar ba,” in ji Mukhtar Shagari.
Shagari ya ƙara da cewa kamar yadda kowanne ɗan Nijeriya ke da ‘yancin shiga siyasa, haka ma yana da ‘yancin zaɓar kada ya shiga, yana mai cewa ya kamata a mutunta shawarar Fubara ba tare da yawaita hasashe ba.















Discussion about this post