ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Batun Sauya Sheka Da Makomar Dimokiradiyyar Nijeriya  A 2027

by Leadership Hausa
4 months ago
Sheka

A yayin da Nijeriya ke shirye-shiyen shiga wani sabon zango na tunkarar zabukan shekarar 2027, ‘yan siyasa, masu rike da madafun iko, sai  kai Gwauro da Mari suke ta faman yi, domin ci gaba da rike ikonsu, inda wasun su kuma suke ta sauya sheka zuwa wasu jamiyyu, domin dai, su ga sun tsallake siradin, na 2027.

Koda yake, wannan halin, ba sabon abu ne, fannin siyasar kasar ba, amma abinda yake sabo ga batun shi ne, ganin yadda kota halin kaka, masu rike da madafun ikon, suke son ci gaba da rike madafun na su, na ikon.

  • Majalisar Dattawa Ta Kai Ta’aziyya Ga Al’ummar Kurmin Wali, Ta Yi Alkawarin Kayan Agaji
  • Hotuna: Babbar Mota Ta Hallaka Wata Bafulatana A Bauchi

Akasarin wadannan ‘yan siyasar da ke a cikin jami’yyun adawa, na dai ganin sauya sheka zuwa jami’iyya mai mulki, shi ne, kawai mafita, a gare su, matukar suna son ci gaba da jan ragamar alumominsu, da suka jagoranta.

ADVERTISEMENT

Misali, akalla Gwamnonin hudu na jam’iyyar PDP, a  watan Disambar 2025, suka sauya sheka, inda suka danganta cewa, sun yi hakan ne, saboda rikice-rikiecen cikin gida, a PDP, inda daga baya, wasu Gwamnoni biyu, suma, suka bi sahu.

Kazalika, sauya sheka da Gwamnan jihar Knao da aka zaba a inuwar jam’iyyar NNPP zuwa jami’iyyar APC, hakan ya kawo karshen rade-radin da ake yi, cewa, Abba Kabir Yusuf, zai sauya sheka.

LABARAI MASU NASABA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Za a dai iya cewa, a jamhuriya ta hudu, akasarin tsare-tsare da sauran shiye-shiye irin na shugabanci a tsakanin jam’iyyu, kusan duk sun kau.

Hakan ya sanya, jami’iyyun tamkar su zamo  wani Tsani na kawai neman takara da tattaunawa tare da hada-hadar Tikitin neman tsayawa takara.

A gafe daya kuma, an shafe shekaru, kotuna na shiga tsakanin jami’iyyu, idan an samu wata takaddama, a yayin da aka gudanar da zabukan fidda gwani.

A saboda kaucewa duk wani tirniki, da ‘yan siyasa, musamman ‘yan takara suke ganin za su fuskanta, hakan ya sanya, suke kokarin sauya sheka, domin samun kai wa, ga tudun mun tsira.

Mulkin Dimokiradiyya dai, ya dogara ne kachokam, kan sasantawa a cikin sauki, a tsakanin ‘yan takara, inda su kuma masu kada kuri’a ke barge gumisnu, ta hanyar zabar wanda suke ra’yi, a ranar zabe.

Hakazalika, a daidai lokacin da zabukan 2027 ke kara karatowa, inda a lokacin ne, ‘yan Nijeriya ya kamata su yanke hukuncin wanda ya fi cancanta ya shugabance su, amma abin takaici, sai dai kawai, ‘yan siyasar, su shige daki su yi kukus kan wanda zai tsaya takara, ba tare da gudanar da yin yakin neman zabe ba.

Wannan ya kara haifar da rashin amincewa, a zuciyar ‘yan kasar da kuma kara durkuasar da Dimokiradiyyar kasar.

Kazalika, a kasar akwai matsin tattalin arziki da rashin gamsuwa, musamman a tsakanin matasa, wanda hakan ke haifar da rauni, ga sakamakon zabe.

Mai makon ‘yan siyasar su rinka janyo masu jefa kuri’a a jiki da nuna gaskiya, amma sun buge da sauya sheka, zuwa wata jami’yya.

Wannan yawan sauya shekar, na janyo babbar illa ga tsari da akidar samar da ci gaba a kasa.

Hakazalika, ba wai lallai sai bangaren shari’a, ya shiga tsakanin duk wata takadda da ta kunno kai a cikin jam’iyyu ba, domin abu ne, su jami’iyyun za su iya lalubo da mafita.

Shigar da bangaren shari’a a duk wata tataburza ta rikicin da ya kunno kai a cikin wata jami’iyya hakan kan shafi kima da kuma martabar bangren na shari’a, inda hakan zai kuma zubar da mutucin bangaren, a idon ‘yan kasa.

Nijeriya dai, ba za iya samar da kinshikin Dimokiradiyya mai dore ba, matukar,  ‘yan siyasar kasar, za su ci gaba da sauya sheka, zuwa wata jami’yya.

Ya zama wajbi, jami’yyun kasar su tabbatar da sun karfafa Dimokiradiyya a cikin jami’yyunsu da kara karfafa kundin tsarin mulkin jami’iyyunsu, tare da daukar mataki, ga duk ‘yan jami’yyar da suka sauya sheka.

Dole a rinka yin gaskiya a yayin zaben fidda gwani kuma dole ‘ya’yan jami’iyyun su san da cewa, suna da hakki a yayin gudanar zaben fidda gwani, jami’iyyunsu.

Bugu da kari, suma sauran hukumomin da ke sanya ido, a kasar, akiwar rawar da za su iya takawa, kan batun.

Wabi ne batun sauye-sayen dokar zabe, ta wuce batu ne na tabbatar da ladarbarwa da cikn ka’ida, a tsakanin jam’iyyu.

Bayar da ‘yanci fadar ra’ayi ga kungiyoyi, abu ne da ke da matukar mahaimmanci, domin idan babu hakan, akwai matsala.

Mulin Dimokiradiyya na ginawa ne kawai, daga bangaren masu kada kuri’a, ba wai a tsakanin ‘yan siyasa, su kadai ba.

Zabukan na 2027, za su kasance tamkar gwajin dafi ne, ga jami’iyyun kasar, inda hukuncin da jami’yyun da ‘yan siyasa da kutuna da kuma masu kada kuri’a, za su kan wanda wanda zai samu nasara.

Irin wannan salon na sauya sheka, matukar ba a dauki matakan da suka kamata ba, hakan ko dai ya haifar da alfanu na gajeren zango ko ma, na dogon zango.

Nijiya dai, na cikin tsaka mai wuya, dangane da zabukan na 2027, da ke kara karatowa.

Alamu dai na nuna cewa, irin wannan sauya shekar da ‘yan siyasar ke ci gaba da yi, akwai yuwuar, za a jingine batun ‘yancin masu jefa kuri’a.

Sheka
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
Manyan Labarai

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Next Post
Ba Zamu Lamunci Buƙatar Murabus Ɗin Mataimakin Gwamna Ba — Kwankwasiyya

Ba Zamu Lamunci Buƙatar Murabus Ɗin Mataimakin Gwamna Ba — Kwankwasiyya

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.