ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Batun Sauya Sheka Da Makomar Dimokiradiyyar Nijeriya  A 2027

by Leadership Hausa
6 months ago
Sheka

A yayin da Nijeriya ke shirye-shiyen shiga wani sabon zango na tunkarar zabukan shekarar 2027, ‘yan siyasa, masu rike da madafun iko, sai  kai Gwauro da Mari suke ta faman yi, domin ci gaba da rike ikonsu, inda wasun su kuma suke ta sauya sheka zuwa wasu jamiyyu, domin dai, su ga sun tsallake siradin, na 2027.

Koda yake, wannan halin, ba sabon abu ne, fannin siyasar kasar ba, amma abinda yake sabo ga batun shi ne, ganin yadda kota halin kaka, masu rike da madafun ikon, suke son ci gaba da rike madafun na su, na ikon.

  • Majalisar Dattawa Ta Kai Ta’aziyya Ga Al’ummar Kurmin Wali, Ta Yi Alkawarin Kayan Agaji
  • Hotuna: Babbar Mota Ta Hallaka Wata Bafulatana A Bauchi

Akasarin wadannan ‘yan siyasar da ke a cikin jami’yyun adawa, na dai ganin sauya sheka zuwa jami’iyya mai mulki, shi ne, kawai mafita, a gare su, matukar suna son ci gaba da jan ragamar alumominsu, da suka jagoranta.

ADVERTISEMENT

Misali, akalla Gwamnonin hudu na jam’iyyar PDP, a  watan Disambar 2025, suka sauya sheka, inda suka danganta cewa, sun yi hakan ne, saboda rikice-rikiecen cikin gida, a PDP, inda daga baya, wasu Gwamnoni biyu, suma, suka bi sahu.

Kazalika, sauya sheka da Gwamnan jihar Knao da aka zaba a inuwar jam’iyyar NNPP zuwa jami’iyyar APC, hakan ya kawo karshen rade-radin da ake yi, cewa, Abba Kabir Yusuf, zai sauya sheka.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Za a dai iya cewa, a jamhuriya ta hudu, akasarin tsare-tsare da sauran shiye-shiye irin na shugabanci a tsakanin jam’iyyu, kusan duk sun kau.

Hakan ya sanya, jami’iyyun tamkar su zamo  wani Tsani na kawai neman takara da tattaunawa tare da hada-hadar Tikitin neman tsayawa takara.

A gafe daya kuma, an shafe shekaru, kotuna na shiga tsakanin jami’iyyu, idan an samu wata takaddama, a yayin da aka gudanar da zabukan fidda gwani.

A saboda kaucewa duk wani tirniki, da ‘yan siyasa, musamman ‘yan takara suke ganin za su fuskanta, hakan ya sanya, suke kokarin sauya sheka, domin samun kai wa, ga tudun mun tsira.

Mulkin Dimokiradiyya dai, ya dogara ne kachokam, kan sasantawa a cikin sauki, a tsakanin ‘yan takara, inda su kuma masu kada kuri’a ke barge gumisnu, ta hanyar zabar wanda suke ra’yi, a ranar zabe.

Hakazalika, a daidai lokacin da zabukan 2027 ke kara karatowa, inda a lokacin ne, ‘yan Nijeriya ya kamata su yanke hukuncin wanda ya fi cancanta ya shugabance su, amma abin takaici, sai dai kawai, ‘yan siyasar, su shige daki su yi kukus kan wanda zai tsaya takara, ba tare da gudanar da yin yakin neman zabe ba.

Wannan ya kara haifar da rashin amincewa, a zuciyar ‘yan kasar da kuma kara durkuasar da Dimokiradiyyar kasar.

Kazalika, a kasar akwai matsin tattalin arziki da rashin gamsuwa, musamman a tsakanin matasa, wanda hakan ke haifar da rauni, ga sakamakon zabe.

Mai makon ‘yan siyasar su rinka janyo masu jefa kuri’a a jiki da nuna gaskiya, amma sun buge da sauya sheka, zuwa wata jami’yya.

Wannan yawan sauya shekar, na janyo babbar illa ga tsari da akidar samar da ci gaba a kasa.

Hakazalika, ba wai lallai sai bangaren shari’a, ya shiga tsakanin duk wata takadda da ta kunno kai a cikin jam’iyyu ba, domin abu ne, su jami’iyyun za su iya lalubo da mafita.

Shigar da bangaren shari’a a duk wata tataburza ta rikicin da ya kunno kai a cikin wata jami’iyya hakan kan shafi kima da kuma martabar bangren na shari’a, inda hakan zai kuma zubar da mutucin bangaren, a idon ‘yan kasa.

Nijeriya dai, ba za iya samar da kinshikin Dimokiradiyya mai dore ba, matukar,  ‘yan siyasar kasar, za su ci gaba da sauya sheka, zuwa wata jami’yya.

Ya zama wajbi, jami’yyun kasar su tabbatar da sun karfafa Dimokiradiyya a cikin jami’yyunsu da kara karfafa kundin tsarin mulkin jami’iyyunsu, tare da daukar mataki, ga duk ‘yan jami’yyar da suka sauya sheka.

Dole a rinka yin gaskiya a yayin zaben fidda gwani kuma dole ‘ya’yan jami’iyyun su san da cewa, suna da hakki a yayin gudanar zaben fidda gwani, jami’iyyunsu.

Bugu da kari, suma sauran hukumomin da ke sanya ido, a kasar, akiwar rawar da za su iya takawa, kan batun.

Wabi ne batun sauye-sayen dokar zabe, ta wuce batu ne na tabbatar da ladarbarwa da cikn ka’ida, a tsakanin jam’iyyu.

Bayar da ‘yanci fadar ra’ayi ga kungiyoyi, abu ne da ke da matukar mahaimmanci, domin idan babu hakan, akwai matsala.

Mulin Dimokiradiyya na ginawa ne kawai, daga bangaren masu kada kuri’a, ba wai a tsakanin ‘yan siyasa, su kadai ba.

Zabukan na 2027, za su kasance tamkar gwajin dafi ne, ga jami’iyyun kasar, inda hukuncin da jami’yyun da ‘yan siyasa da kutuna da kuma masu kada kuri’a, za su kan wanda wanda zai samu nasara.

Irin wannan salon na sauya sheka, matukar ba a dauki matakan da suka kamata ba, hakan ko dai ya haifar da alfanu na gajeren zango ko ma, na dogon zango.

Nijiya dai, na cikin tsaka mai wuya, dangane da zabukan na 2027, da ke kara karatowa.

Alamu dai na nuna cewa, irin wannan sauya shekar da ‘yan siyasar ke ci gaba da yi, akwai yuwuar, za a jingine batun ‘yancin masu jefa kuri’a.

Sheka
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Next Post
Ba Zamu Lamunci Buƙatar Murabus Ɗin Mataimakin Gwamna Ba — Kwankwasiyya

Ba Zamu Lamunci Buƙatar Murabus Ɗin Mataimakin Gwamna Ba — Kwankwasiyya

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.