Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Bauchi ta ayyana ɓarkewar cutar kwalara a jihar bayan gwaje-gwaje sun tabbatar da samuwar cutar, tare da ƙaruwa a yawan mutanen da ake zargin sun kamu da ita a sassa daban-daban na jihar.
Ma’aikatar ta ce zuwa ranar 31 ga Yuli, 2026, an samu mutane 398 da ake zargin sun kamu da cutar a ƙananan hukumomi 13, yayin da mutane 16 suka rasu. Wannan ya nuna adadin mace-macen ya kai kusan kashi huɗu cikin 100 na waɗanda ake zargin sun kamu.
Ƙananan hukumomin da cutar ta fi shafa sun haɗa da Toro mai mutane 231, Alkaleri da Kirfi mai mutane 46 kowacce, Ganjuwa mai mutane 21, da Bauchi da Tafawa Balewa mai mutane 14 kowacce. Haka kuma, ma’aikatar ta ce gwaje-gwajen PCR sun tabbatar da mutane shida sun kamu da ƙwayar Vibrio cholerae O1 Ogawa, lamarin da ya tabbatar da yaɗuwar cutar a jihar.
Kwamishinan Lafiya na jihar, Dakta Sani Mohammed Dambam, ya ce an ayyana ɓarkewar cutar ne bisa shawarwarin masana binciken cututtuka da cibiyar gaggawar kula da lafiyar jama’a, tare da tanade-tanaden Dokokin Kiwon Lafiya na Duniya na shekarar 2005 da sauran ƙa’idojin yaƙi da kwalara.
Ya ce gwamnati ta tura tawagogin gaggawa zuwa ƙananan hukumomin da abin ya shafa, tare da ƙarfafa cibiyoyin kula da marasa lafiya da samar da magunguna da kayan aikin lafiya. Haka kuma, an ƙara sa ido kan cututtuka, samar da tsaftataccen ruwa da tsafta, da wayar da kan jama’a domin dakile yaɗuwar cutar.














