Muhammad Sa’ad Abubakar, Sarkin Musulmi kuma Shugaban Ƙungiyar NSCIA, ya umarci al’ummar Musulmi su fara duban jinjirin watan Ramadan bayan faɗuwar rana a ranar Talata, 17 ga Fabrairu, 2026, wanda ya yi daidai da 29 Sha’aban 1447 A.H. Sanarwar da Babban Sakataren Majalisar, Farfesa. Is-haq Oloyede, ya sanya wa hannu ta bayyana cewa za a dogara da sahihin shaidar ganin wata kafin a ayyana fara azumi.
Majalisar ta ce Kwamitin Duban Wata na Ƙasa, tare da haɗin gwuiwar hukumar lura da sararin samaniyar Nijeriya sun shirya kayan aiki domin tabbatar da ingantacciyar shaida. Idan aka ga jinjirin a daren Talata, za a ayyana Laraba, 18 ga Fabrairu, a matsayin ranar farko ta Ramadan; idan kuma ba a gani ba, Alhamis, 19 ga Fabrairu, za ta zama 1 ga Ramadan 1447 A.H.
- Bukatar Kara Kaimin Ibada A Watan Ramadan
- Majalisa Za Ta Dawo Zama Ranar Talata Kan Wsu Muhimman Batutuwa
Baya ga batun watan azumi, NSCIA ta nuna damuwa kan abin da ta kira ƙaruwar yaɗa labaran kyamar Musulunci a ƙasar cikin shekarar da ta gabata. Ta ce ana ƙoƙarin ɗora wa Musulmi laifuffukan da ba su aikata ba, duk da cewa su ma suna daga cikin waɗanda hare-haren ta’addanci da fashi da makami suka shafa.
Haka kuma, majalisar ta ce ta samu koke-koke bayan da hukumar zabe ta ƙasa ta sanar da cewa za a gudanar da zaɓen shugaban ƙasa a lokacin Ramadan, yayin da zaɓen gwamnoni zai zo kusa da sallar Azumi. Ta ce tana sa ido kan lamarin tare da fatan za a sake nazari kan jadawalin.
NSCIA ta buƙaci Musulmi su kasance masu haƙuri da jajircewa tare da riƙon kyawawan halaye a watan Ramadan, tana addu’ar Allah Ya ba su damar shaida da kammala azumin 1447 A.H cikin koshin lafiya da natsuwa.















Discussion about this post