Majalisar Dokoki ta sanar da cewa majalisar dattawa da ta wakilai za su koma zaman su a ranar Talata, 17 ga Fabrairu, 2026 da misalin ƙarfe 11 na safe. Magatakardar Majalisar, Kamoru Ogunlana, ya buƙaci sanatoci da ’yan majalisa su daidaita jadawalinsu domin cikakken halarta, yana mai cewa za a yanke muhimman shawarwari a kowace majalisa.
Ba a bayyana takamaiman batutuwan da za a tattauna ba. Sai dai an dakatar da zaman a baya domin bai wa ma’aikatu da hukumomi damar kare kasafin kuɗin 2026 da suka gabatar.
- Kwamitin Kolin JKS Da Majalisar Gudanarwar Kasar Sun Gudanar Da Taron Murnar Bikin Bazara
- Majalisar Dattawa Za Ta Yi Zaman Gaggawa Ranar Talata
Rahotanni sun nuna cewa majalisar wakilai na iya yin zama na gaggawa domin duba batutuwan da suka shafi gyaran Dokar Zaɓe, bayan fitar da jadawalin zaɓen 2027 da INEC ta yi.
Jadawalin ya haifar da muhawara kan yiwuwar karo da watan Ramadan na 2027, lamarin da ya sa wasu ’yan majalisa da ’yan ƙasa ke kira da a yi nazari kan sauya wasu ranaku. Ana sa ran zaman na Talata zai yi duba kan yiwuwar daidaita jadawalin domin kauce wa cikas ga ayyukan zaɓe.















Discussion about this post