ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi 2027: Kungiya Ta Fara Nema Wa Farfesa Pate Kuri’a

by Leadership Hausa
8 months ago

Khalid Idris Doya

Wata kungiya mai suna, ‘Professor Pate Grassroots Mobement’ ta fara shiga lungu da sako domin neman wa ministan lafiya, Farfesa Ali Muhammad Pate kuri’a gabanin zaben kujerar gwamnan jihar Bauchi a zaben 2027.

Shugagan kungiyar, Nazeef Sa’id Wambai, a yayin taron tuntuba da neman goyon bayan al’ummar gundumar Makama Sarkin Baki, ya shaida cewar akwai bukatar jama’a su fito su kada kuri’a domin zaben shugaban da ya dace kuma ya cancanta a yayin zaben 2027 da ke tafe.

ADVERTISEMENT
  • Buƙatar A Sake Duba Sabuwar Dokar Haraji
  • Bankwana Da 2025, Maraba Da 2026

Ya ce al’ummar karkara su na gayar bukatar kyakkyawar shugabanci ta yadda za a samar musu da ababen more rayuka kamar su lafiya, tsaro, asibitoci, ruwa, hanyoyi da kuma kayan amfanin gona ba wai manyan motoci ko dima-diman gine-gine ba.

“Muna kan shiga kwararo-kwararo domin wayar wa jama’a kai dangane da ‘yancinsu kan yadda za su matsa kaimi wajen ganin an biya musu bukatunsu ta hanyar shiga a dama da su wajen zaban shugabannin da suka dace. Mun tattauna da kungiyoyin mata, maza, matasa, ‘yan kasuwa da masu sana’ar hannu wadanda matsalolin da ake fuskanta ya damesu kuma suke neman a kawo mai share musu hawaye.

LABARAI MASU NASABA

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

“Sun shaida mana cewar babu ko asibiti guda daya a wannan gundumar. Kuma wannan gundumar na daga cikin manyan gundumomi a jihar Bauchi. Hakan na nuni da cewa suna zuwa wasu wuraren kenan domin neman lafiya. Muna son mu tunkari hukumomin da abun ya shafa kan wannan batun.”

Wambai ya ce Farfesa Muhammad Ali Pate a shirye yake wajen shawo kan matsalolin da suke addabar al’ummomin da suke jihar Bauchi wanda ke da kwarewa sosai a bangaren kiwon lafiya da sauran bangarori. Ya nemi al’ummar jihar da su mara wa Ali Pate baya a zaben 2027 domin ya kai ga shawo matsalolin da suke fuskantar jihar.

Daya daga cikin mazauna gundumar, Jamilu Aminu Gali, ya nuna aniyarsu na mara wa kungiyar baya, ya ce zauna da su domin jin matsalolinsu zai taimaka wajen ganin an kula da halin da suke ciki. Ya ce ba su da asibiti a gundumar hakan na janyowa suke shan wahala wajen daukan masu juna biyu zuwa asibitocin da ke kusa da su.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?
  • Leadership Hausa
    An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

MASU ALAKA

Labarai

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Labarai

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
Next Post
NSCDC Ta Kama Mutane 3 Kan Kisan Jami’inta A Kano

NSCDC Ta Kama Mutane 3 Kan Kisan Jami’inta A Kano

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.