• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Gombe Za Ta Tallafa Wa Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Funakaye

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Kananan Labarai
0
Gwamnatin Gombe Za Ta Tallafa Wa Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Funakaye
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tawagar gwamnatin jihar Gombe karkashin jagorancin kwamishinan da ke sanya ido a ma’aikatar muhalli da gandun daji, Shehu Ibrahim Madugu, ta ziyarci wasu al’ummomin da ambaliyar ruwa ta shafa a garin Bajoga da ke karamar hukumar Funakaye.

Ziyarar ta’aziyya da tantance barnar da tawagar gwamnatin jihar ta kai ya biyo bayan umarnin da gwamna Muhammad Inuwa Yahaya, ya bayar ga ma’aikatar muhallin da hukumar bada agajin gaggawa ta jihar (SEMA) da hukumomin da abin ya shafa kan gaggauta ziyar tare da tantance irin barnar da ambaliyar ta yi, tare da bada tallafi ga wadanda ibtila’in ya shafa don saukaka musu radadi.

  • NBC Ta Ci Tarar Trust TV Tarar Miliyan 5 Kan Yada Ayyukan ‘Yan Bindiga 
  • Yajin Aikin ASUU: Kungiyar Dalubai Ta Bukaci A Kori Ministan Ilimi

Sauran ‘yan tawagar gwamnatin jihar sun hada da kwamishinan tsaron cikin gida da kyautata tarbiyya, Adamu Dishi Kupto, da babban sakataren ma’aikatar muhalli, Ibrahim Sule Bage da wakilin hukumar bada agajin gaggawa (SEMA) da sauransu.

Tawagar ta samu tarba daga shugaban karamar hukumar Funakaye, Alhaji Ibrahim Cheldu da sauran masu ruwa da tsaki wadanda suka zagaya da su yankunan da lamarin ya shafa.

A jawabinsa yayin ziyarar, kwamishina Shehu Ibrahim Madugu, ya mika sakon ta’aziyya da jajantawa na gwamna Inuwa Yahaya, bisa asarar rayuka da dukiyoyi da ambaliyar ta shafa a karamar hukumar.

Labarai Masu Nasaba

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya

“Makasudin zuwanmu a yau shi ne mu jajanta tare da mika ta’aziyyarmu gare ku bisa wannan ibtila’in daya shafe ku, tare da tantance barnar da ambaliyar ta haifar da nufin bai wa gwamnati shawara don samar da tallafi ga wadanda lamarin ya shafa”.

Sai ya bukaci al’ummomin da ke fuskantar matsalar ambaliya su yi biyayya ga hasashen ambaliyar ruwa da gargadin da Hukumar Kula da Yanayi ta Nijeriya (NIMET) ta yi.

A nasa jawabin, shugaban karamar hukumar Funakaye, Ibrahim Adamu Cheldu, ya yaba wa gwamna Inuwa Yahaya, bisa umarnin gaggawa da ya bayar wajen taimaka wa wadanda abin ya shafa tare da bada tabbacin majalisarsa cewa a shirye take ta mara wa gwamnatin jihar baya a kowane lokaci.

Tawagar ta kuma ziyarci Mai Martaba Sarkin Funakaye, Alhaji Muazu Mohammed Kwairanga tare da jajanta masa bisa ibtila’in daya samu al’ummar tasa.

Idan za a iya tunawa wani yaro dan shekaru uku ya rasu yayin da dan uwansa dan shekaru biyu ya samu munanan raunuka sakamakon mamakon ruwan sama da ya yi barna a wasu yankunan garin Bajoga da suka hada da Shara-Mansur da Bodoriyel.

Yankunan da aka ziyarta sun hada da Shara Mansur, da Jillahi da dai sauransu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ambaliyar RuwaGwamna Inuwa MohammedGwamnatin GombeMamakon Ruwan SamaTallafi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Za A Gudanar Da Taron Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Na Duniya Na Shekarar 2022 A Shanghai

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makarantar Tarayya, Sun Kashe Mahaifin Wakilin NAN A Kaduna 

Related

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa
Kananan Labarai

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

4 months ago
Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya
Kananan Labarai

Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya

5 months ago
Ƙarin Harajin Amurka Zai Illata Tattalin Arziƙin Duniya
Kananan Labarai

Ƙarin Harajin Amurka Zai Illata Tattalin Arziƙin Duniya

5 months ago
Gwamnati Ta Amince Da Bai Wa Jami’o’i 11 Masu Zaman Kansu Lasisi
Kananan Labarai

Gwamnati Ta Amince Da Bai Wa Jami’o’i 11 Masu Zaman Kansu Lasisi

6 months ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Kananan Labarai

Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Dala Tiriliyan 7 A Tsarin Kasuwancin Musulunci Na Duniya

12 months ago
Gwamna Dauda Ya Ƙaddamar Da Aikin Sake Gina Asibitin Talata Mafara
Labarai

Gwamna Dauda Ya Ƙaddamar Da Aikin Sake Gina Asibitin Talata Mafara

1 year ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makarantar Tarayya, Sun Kashe Mahaifin Wakilin NAN A Kaduna 

'Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makarantar Tarayya, Sun Kashe Mahaifin Wakilin NAN A Kaduna 

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.