ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Dakile Harin ISWAP Da Boko Haram A Borno

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
5 months ago
ISWAP

Sojojin Rundunar Hadin Gwiwa, Operation HADIN KAI, sun dakile harin da ake zargin ‘yan Boko Haram da ISWAP ne suka kai a kauyuka Pulka da Mandaragirau na Jihar Borno.

A cewar wata sanarwa da Jami’in Sadarwa na Operation HADIN KAI, Laftanar Kanar Sani Uba, ya fitar a ranar Litinin, harin ya faru a ranar Asabar, lokacin da ‘yan ta’addan suka yi kokarin mamaye matsugunan sojoji a wuraren biyu.

  • Sin Ta Ba Da Shawarar Tsayawa Kan Ra’ayoyin Bai Daya Guda Biyar Don Warware Rikicin Sudan
  • Hukumar RUWASSA Ta Kudiri Aniyar Samar Da Ruwa A Fadin Jihar Katsina

Sojoji sun bayyana cewa ‘yan ta’addan da ke ci gaba daga yankin daji na Sambisa sun kai mummunan harin kan sojojin Sashen 1 a Pulka. Duk da haka, sojoji sun fafata da masu kai harin da aka bayyana da yaki mai tsanani, inda suka sami nasarar dakile harin da kuma mayar da ‘yan ta’addan baya.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta kara da cewa, kodayake an samu wani Bangare na shingen tsaro da aka dan karya na dan lokaci wanda ya haifar da lalacewar wasu kayan yaki da wuraren masauki, saurin karin sojoji daga rundunar 26 Brigade ya tilasta ‘yan ta’addan su janye zuwa yankin Sambisa.

“Sahihin Bincike ya nuna cewa ‘yan ta’addan sun yi asarar rayuka sosai, ciki har da babban kwamanda da aka gano mai suna Abou Aisha wanda ya samu mummunan raunin bindiga a wuya har ya rasu, tare da babbar asarar makamai da kayan aiki,” in ji sanarwar.

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

Sojojin sun kara da cewa babu wani dan soji da ya rasa ransa yayin fafatawar a Pulka.

A wani labari da ya shafi wannan, an ruwaito cewa sojojin Sashen 2 a Mandaragirau sun shiga wani harin da aka tsara sosai daga Bangarori da dama da ‘yan ISWAP suka kai, wadanda suka hau manyan motoci masu makami da babura. Sanarwar ta bayyana cewa sojoji sun tsara kungiyoyin yaki a wuraren da suka dace domin dakile irin wadannan hare-hare, inda suka samu nasarar korar masu kai harin bayan doguwar musayar wuta.

Duk da cewa shingen wurin bai karye ba, sojojin sun amince cewa wasu sojoji da mambobin CiBilian Joint Task Force sun rasa rayukansu a wannan karo. Wasu da suka ji rauni an tura su da sashin jiragen sama na Operation HADIN KAI da kuma jiragen sojin kasa zuwa asibitoci domin samun kulawar likitoci.

“Sadaukarwarsu tana nuna manyan dabi’un aiki, jarumtaka, da kwazo wajen kare Nijeriya,” in ji sanarwar.

Haka kuma, rundunar ta bayyana cewa ayyukan bincike a kan hanyar Kimba sun gano sawun jini, kaburbura kasa da kasa, da kayan da aka bari a wurin, yayin da shaidun gani da ido suka nuna cewa an ceto wasu ‘yan ta’adda da suka ji rauni daga filin fama.

Manyan kwamandojin rundunar sun yaba wa sojojin bisa kwarewa da juriya, inda suka bayyana cewa gazawar hare-haren ya nuna karuwar matsin lamba ga kungiyoyin ‘yan ta’adda da ke aiki a Arewa-Maso-Gabas.

Operation HADIN KAI ta sake jaddada kudurinta na tarwatsa kungiyoyin ‘yan ta’adda da dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

ISWAP
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
ISWAP
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai
  • Sulaiman
    Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
  • Sulaiman
    Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma
  • Sulaiman
    Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tsaro

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

July 11, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’
Tsaro

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Next Post
Ramadan: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci Ga Limamai 40 A Zamfara

Ramadan: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci Ga Limamai 40 A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.