ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Dakile Harin ISWAP Da Boko Haram A Borno

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
3 months ago
ISWAP

Sojojin Rundunar Hadin Gwiwa, Operation HADIN KAI, sun dakile harin da ake zargin ‘yan Boko Haram da ISWAP ne suka kai a kauyuka Pulka da Mandaragirau na Jihar Borno.

A cewar wata sanarwa da Jami’in Sadarwa na Operation HADIN KAI, Laftanar Kanar Sani Uba, ya fitar a ranar Litinin, harin ya faru a ranar Asabar, lokacin da ‘yan ta’addan suka yi kokarin mamaye matsugunan sojoji a wuraren biyu.

  • Sin Ta Ba Da Shawarar Tsayawa Kan Ra’ayoyin Bai Daya Guda Biyar Don Warware Rikicin Sudan
  • Hukumar RUWASSA Ta Kudiri Aniyar Samar Da Ruwa A Fadin Jihar Katsina

Sojoji sun bayyana cewa ‘yan ta’addan da ke ci gaba daga yankin daji na Sambisa sun kai mummunan harin kan sojojin Sashen 1 a Pulka. Duk da haka, sojoji sun fafata da masu kai harin da aka bayyana da yaki mai tsanani, inda suka sami nasarar dakile harin da kuma mayar da ‘yan ta’addan baya.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta kara da cewa, kodayake an samu wani Bangare na shingen tsaro da aka dan karya na dan lokaci wanda ya haifar da lalacewar wasu kayan yaki da wuraren masauki, saurin karin sojoji daga rundunar 26 Brigade ya tilasta ‘yan ta’addan su janye zuwa yankin Sambisa.

“Sahihin Bincike ya nuna cewa ‘yan ta’addan sun yi asarar rayuka sosai, ciki har da babban kwamanda da aka gano mai suna Abou Aisha wanda ya samu mummunan raunin bindiga a wuya har ya rasu, tare da babbar asarar makamai da kayan aiki,” in ji sanarwar.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi

NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano

Sojojin sun kara da cewa babu wani dan soji da ya rasa ransa yayin fafatawar a Pulka.

A wani labari da ya shafi wannan, an ruwaito cewa sojojin Sashen 2 a Mandaragirau sun shiga wani harin da aka tsara sosai daga Bangarori da dama da ‘yan ISWAP suka kai, wadanda suka hau manyan motoci masu makami da babura. Sanarwar ta bayyana cewa sojoji sun tsara kungiyoyin yaki a wuraren da suka dace domin dakile irin wadannan hare-hare, inda suka samu nasarar korar masu kai harin bayan doguwar musayar wuta.

Duk da cewa shingen wurin bai karye ba, sojojin sun amince cewa wasu sojoji da mambobin CiBilian Joint Task Force sun rasa rayukansu a wannan karo. Wasu da suka ji rauni an tura su da sashin jiragen sama na Operation HADIN KAI da kuma jiragen sojin kasa zuwa asibitoci domin samun kulawar likitoci.

“Sadaukarwarsu tana nuna manyan dabi’un aiki, jarumtaka, da kwazo wajen kare Nijeriya,” in ji sanarwar.

Haka kuma, rundunar ta bayyana cewa ayyukan bincike a kan hanyar Kimba sun gano sawun jini, kaburbura kasa da kasa, da kayan da aka bari a wurin, yayin da shaidun gani da ido suka nuna cewa an ceto wasu ‘yan ta’adda da suka ji rauni daga filin fama.

Manyan kwamandojin rundunar sun yaba wa sojojin bisa kwarewa da juriya, inda suka bayyana cewa gazawar hare-haren ya nuna karuwar matsin lamba ga kungiyoyin ‘yan ta’adda da ke aiki a Arewa-Maso-Gabas.

Operation HADIN KAI ta sake jaddada kudurinta na tarwatsa kungiyoyin ‘yan ta’adda da dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

ISWAP
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya
ISWAP
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

MASU ALAKA

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi

June 1, 2026
NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
Tsaro

NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano

May 31, 2026
Yadda Muka Kashe Masu Garkuwa 4 Da Suke Shirin Kai Hari Kan Attajirai A Legas —CP
Tsaro

Yadda Muka Kashe Masu Garkuwa 4 Da Suke Shirin Kai Hari Kan Attajirai A Legas —CP

May 31, 2026
Next Post
Ramadan: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci Ga Limamai 40 A Zamfara

Ramadan: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci Ga Limamai 40 A Zamfara

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.