ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Dakile Harin ISWAP Da Boko Haram A Borno

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
7 months ago
ISWAP

Sojojin Rundunar Hadin Gwiwa, Operation HADIN KAI, sun dakile harin da ake zargin ‘yan Boko Haram da ISWAP ne suka kai a kauyuka Pulka da Mandaragirau na Jihar Borno.

A cewar wata sanarwa da Jami’in Sadarwa na Operation HADIN KAI, Laftanar Kanar Sani Uba, ya fitar a ranar Litinin, harin ya faru a ranar Asabar, lokacin da ‘yan ta’addan suka yi kokarin mamaye matsugunan sojoji a wuraren biyu.

  • Sin Ta Ba Da Shawarar Tsayawa Kan Ra’ayoyin Bai Daya Guda Biyar Don Warware Rikicin Sudan
  • Hukumar RUWASSA Ta Kudiri Aniyar Samar Da Ruwa A Fadin Jihar Katsina

Sojoji sun bayyana cewa ‘yan ta’addan da ke ci gaba daga yankin daji na Sambisa sun kai mummunan harin kan sojojin Sashen 1 a Pulka. Duk da haka, sojoji sun fafata da masu kai harin da aka bayyana da yaki mai tsanani, inda suka sami nasarar dakile harin da kuma mayar da ‘yan ta’addan baya.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta kara da cewa, kodayake an samu wani Bangare na shingen tsaro da aka dan karya na dan lokaci wanda ya haifar da lalacewar wasu kayan yaki da wuraren masauki, saurin karin sojoji daga rundunar 26 Brigade ya tilasta ‘yan ta’addan su janye zuwa yankin Sambisa.

“Sahihin Bincike ya nuna cewa ‘yan ta’addan sun yi asarar rayuka sosai, ciki har da babban kwamanda da aka gano mai suna Abou Aisha wanda ya samu mummunan raunin bindiga a wuya har ya rasu, tare da babbar asarar makamai da kayan aiki,” in ji sanarwar.

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

Sojojin sun kara da cewa babu wani dan soji da ya rasa ransa yayin fafatawar a Pulka.

A wani labari da ya shafi wannan, an ruwaito cewa sojojin Sashen 2 a Mandaragirau sun shiga wani harin da aka tsara sosai daga Bangarori da dama da ‘yan ISWAP suka kai, wadanda suka hau manyan motoci masu makami da babura. Sanarwar ta bayyana cewa sojoji sun tsara kungiyoyin yaki a wuraren da suka dace domin dakile irin wadannan hare-hare, inda suka samu nasarar korar masu kai harin bayan doguwar musayar wuta.

Duk da cewa shingen wurin bai karye ba, sojojin sun amince cewa wasu sojoji da mambobin CiBilian Joint Task Force sun rasa rayukansu a wannan karo. Wasu da suka ji rauni an tura su da sashin jiragen sama na Operation HADIN KAI da kuma jiragen sojin kasa zuwa asibitoci domin samun kulawar likitoci.

“Sadaukarwarsu tana nuna manyan dabi’un aiki, jarumtaka, da kwazo wajen kare Nijeriya,” in ji sanarwar.

Haka kuma, rundunar ta bayyana cewa ayyukan bincike a kan hanyar Kimba sun gano sawun jini, kaburbura kasa da kasa, da kayan da aka bari a wurin, yayin da shaidun gani da ido suka nuna cewa an ceto wasu ‘yan ta’adda da suka ji rauni daga filin fama.

Manyan kwamandojin rundunar sun yaba wa sojojin bisa kwarewa da juriya, inda suka bayyana cewa gazawar hare-haren ya nuna karuwar matsin lamba ga kungiyoyin ‘yan ta’adda da ke aiki a Arewa-Maso-Gabas.

Operation HADIN KAI ta sake jaddada kudurinta na tarwatsa kungiyoyin ‘yan ta’adda da dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

ISWAP
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas
ISWAP
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tsaro

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

July 11, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’
Tsaro

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Next Post
Ramadan: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci Ga Limamai 40 A Zamfara

Ramadan: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci Ga Limamai 40 A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.