Rundunar Ƴansanda ta Jihar Legas ta bayyana yadda jami’anta suka daƙile yunƙurin garkuwa da mutane tare da kashe wasu da ake zargi ƴan bindiga huɗu a wata arangama da ta faru a yankin Ejigbo.
Kwamishinan ƴansandan Jihar, Tijani Fatai, ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da aka gudanar a hedikwatar rundunar da ke Ikeja.
Ya ce lamarin ya faru ne a ranar 24 ga Mayu, 2026, da misalin ƙarfe 9:30 na dare, bayan samun sahihan bayanan sirri kan shirin yin garkuwa da wani ɗan kasuwa a ƙofar Jakande Estate da ke yankin Ejigbo.
CP Fatai ya ce ƴan bindigar suna cikin wata shahararriyar ƙungiya da ke kai hari kan attajirai da ƴan kasuwa masu kuɗi a duk lokacin da suka shiga Jihar Legas domin aikata laifi.
Ya ƙara da cewa bincike ya nuna cewa shugaban ƙungiyar, wanda aka fi sani da Ifeanyi ko “Ifeko”, ya horar da wani Henry Asoona, wanda shi ma ake zargin jagoran wata ƙungiyar garkuwa da attajirai da aka taɓa murƙushewa a kasuwar Ladipo a shekarar 2024.
A cewarsa, Ifeanyi yana zaune a ƙasashen waje amma ya dawo Legas domin tsara wannan aikin garkuwa da mutane.
Ya ce da suka hango ƴansanda, ƴan bindigar suka buɗe wuta, inda aka shiga musayar wuta mai zafi tsakaninsu da jami’an tsaro.
“Jami’anmu sun mayar da martani da ƙarfi, wanda ya kai ga hallaka mutum huɗu daga cikin su, yayin da ɗaya ya tsere da raunin harbi,” in ji shi.
Rundunar ta ce an kuma gano kayayyaki da dama daga wurin, ciki har da mota ƙirar Toyota Sienna, bindiga AK-47 guda ɗaya da harsashi 25, bindiga SMG da harsashi 12, da kuma makullan motoci ƙirar Toyota Corolla da Leɗus.
CP ɗin ya ƙara da cewa wani jami’in ƴansanda ya samu rauni a ƙafa yayin musayar wutar, kuma yana karɓar magani a asibiti.
Ya ce bincike na ci gaba domin kamo wanda ya tsere da sauran abokan aikinsu.
Haka kuma ya bayyana cewa rundunar ta kama wasu mutum 10 a cikin watan Mayu saboda laifuka daban-daban, tare da ƙwato makamai da abubuwa masu haɗari.
A ƙarshe, ya tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da amfani da bayanan sirri da dabarun aiki domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi a faɗin Jihar Legas.















Discussion about this post