ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Muka Kashe Masu Garkuwa 4 Da Suke Shirin Kai Hari Kan Attajirai A Legas —CP

by Abubakar Sulaiman
2 months ago

Rundunar Ƴansanda ta Jihar Legas ta bayyana yadda jami’anta suka daƙile yunƙurin garkuwa da mutane tare da kashe wasu da ake zargi ƴan bindiga huɗu a wata arangama da ta faru a yankin Ejigbo.

Kwamishinan ƴansandan Jihar, Tijani Fatai, ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da aka gudanar a hedikwatar rundunar da ke Ikeja.

Ya ce lamarin ya faru ne a ranar 24 ga Mayu, 2026, da misalin ƙarfe 9:30 na dare, bayan samun sahihan bayanan sirri kan shirin yin garkuwa da wani ɗan kasuwa a ƙofar Jakande Estate da ke yankin Ejigbo.

ADVERTISEMENT

CP Fatai ya ce ƴan bindigar suna cikin wata shahararriyar ƙungiya da ke kai hari kan attajirai da ƴan kasuwa masu kuɗi a duk lokacin da suka shiga Jihar Legas domin aikata laifi.

Ya ƙara da cewa bincike ya nuna cewa shugaban ƙungiyar, wanda aka fi sani da Ifeanyi ko “Ifeko”, ya horar da wani Henry Asoona, wanda shi ma ake zargin jagoran wata ƙungiyar garkuwa da attajirai da aka taɓa murƙushewa a kasuwar Ladipo a shekarar 2024.

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

A cewarsa, Ifeanyi yana zaune a ƙasashen waje amma ya dawo Legas domin tsara wannan aikin garkuwa da mutane.

Ya ce da suka hango ƴansanda, ƴan bindigar suka buɗe wuta, inda aka shiga musayar wuta mai zafi tsakaninsu da jami’an tsaro.

“Jami’anmu sun mayar da martani da ƙarfi, wanda ya kai ga hallaka mutum huɗu daga cikin su, yayin da ɗaya ya tsere da raunin harbi,” in ji shi.

Rundunar ta ce an kuma gano kayayyaki da dama daga wurin, ciki har da mota ƙirar Toyota Sienna, bindiga AK-47 guda ɗaya da harsashi 25, bindiga SMG da harsashi 12, da kuma makullan motoci ƙirar Toyota Corolla da Leɗus.

CP ɗin ya ƙara da cewa wani jami’in ƴansanda ya samu rauni a ƙafa yayin musayar wutar, kuma yana karɓar magani a asibiti.

Ya ce bincike na ci gaba domin kamo wanda ya tsere da sauran abokan aikinsu.

Haka kuma ya bayyana cewa rundunar ta kama wasu mutum 10 a cikin watan Mayu saboda laifuka daban-daban, tare da ƙwato makamai da abubuwa masu haɗari.

A ƙarshe, ya tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da amfani da bayanan sirri da dabarun aiki domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi a faɗin Jihar Legas.

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu
  • Abubakar Sulaiman
    Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano
  • Abubakar Sulaiman
    An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi
  • Abubakar Sulaiman
    Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tsaro

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

July 11, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’
Tsaro

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Next Post
Sin: A Sa Kaimi Ga Yunkurin Tabbatar Da Kwanciyar Hankali A Duniya

Sin: A Sa Kaimi Ga Yunkurin Tabbatar Da Kwanciyar Hankali A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026
Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

July 17, 2026
Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.