ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Muka Kashe Masu Garkuwa 4 Da Suke Shirin Kai Hari Kan Attajirai A Legas —CP

by Abubakar Sulaiman
4 weeks ago

Rundunar Ƴansanda ta Jihar Legas ta bayyana yadda jami’anta suka daƙile yunƙurin garkuwa da mutane tare da kashe wasu da ake zargi ƴan bindiga huɗu a wata arangama da ta faru a yankin Ejigbo.

Kwamishinan ƴansandan Jihar, Tijani Fatai, ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da aka gudanar a hedikwatar rundunar da ke Ikeja.

Ya ce lamarin ya faru ne a ranar 24 ga Mayu, 2026, da misalin ƙarfe 9:30 na dare, bayan samun sahihan bayanan sirri kan shirin yin garkuwa da wani ɗan kasuwa a ƙofar Jakande Estate da ke yankin Ejigbo.

ADVERTISEMENT

CP Fatai ya ce ƴan bindigar suna cikin wata shahararriyar ƙungiya da ke kai hari kan attajirai da ƴan kasuwa masu kuɗi a duk lokacin da suka shiga Jihar Legas domin aikata laifi.

Ya ƙara da cewa bincike ya nuna cewa shugaban ƙungiyar, wanda aka fi sani da Ifeanyi ko “Ifeko”, ya horar da wani Henry Asoona, wanda shi ma ake zargin jagoran wata ƙungiyar garkuwa da attajirai da aka taɓa murƙushewa a kasuwar Ladipo a shekarar 2024.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

A cewarsa, Ifeanyi yana zaune a ƙasashen waje amma ya dawo Legas domin tsara wannan aikin garkuwa da mutane.

Ya ce da suka hango ƴansanda, ƴan bindigar suka buɗe wuta, inda aka shiga musayar wuta mai zafi tsakaninsu da jami’an tsaro.

“Jami’anmu sun mayar da martani da ƙarfi, wanda ya kai ga hallaka mutum huɗu daga cikin su, yayin da ɗaya ya tsere da raunin harbi,” in ji shi.

Rundunar ta ce an kuma gano kayayyaki da dama daga wurin, ciki har da mota ƙirar Toyota Sienna, bindiga AK-47 guda ɗaya da harsashi 25, bindiga SMG da harsashi 12, da kuma makullan motoci ƙirar Toyota Corolla da Leɗus.

CP ɗin ya ƙara da cewa wani jami’in ƴansanda ya samu rauni a ƙafa yayin musayar wutar, kuma yana karɓar magani a asibiti.

Ya ce bincike na ci gaba domin kamo wanda ya tsere da sauran abokan aikinsu.

Haka kuma ya bayyana cewa rundunar ta kama wasu mutum 10 a cikin watan Mayu saboda laifuka daban-daban, tare da ƙwato makamai da abubuwa masu haɗari.

A ƙarshe, ya tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da amfani da bayanan sirri da dabarun aiki domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi a faɗin Jihar Legas.

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
  • Abubakar Sulaiman
    Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi
Tsaro

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

June 19, 2026
Next Post
Sin: A Sa Kaimi Ga Yunkurin Tabbatar Da Kwanciyar Hankali A Duniya

Sin: A Sa Kaimi Ga Yunkurin Tabbatar Da Kwanciyar Hankali A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026
Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.