ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Kudiri Aniyar Bunkasa Sana’ar Kiwon Dabbobi Ta Mata —Minista

by Leadership Hausa
7 months ago

Daga Abubakar Abba

Ministan Ma’aikatar Bunkasa Kiwon Dabbobi, Idi Mukhtar Maiha, ya sanar da cewa; gwamnatin tarayya ta sanya kudurinta, wajen bunkasa kiwon dabbobi da matan kasar ke yi.

Ya bayyana haka ne, a hirar da aka yi da shi a Abuja, inda ya ce; mata su ne kashin bayan habaka fannin tattalin arzikin kiwon dabbobi a fadin kasar.

  • NNPP Ta Rushe Shugabancinta A Kano Biyo Bayan Jita-jitar Sauya Sheƙar Abba Zuwa APC
  • Batutuwan Da Suka Ci Wa ‘Yan Adawa Tuwo A Ƙwarya A Siyasar 2025

A cewar ministan, a karkashin shirin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, gwamnatinsa ta daga darajar fannin kiwon dabbobi na kasa da kuma kara samar da dama kan sana’o’in da matan kasar ke gudanarwa, musamman domin matan su bayar da tasu gudanmawar ga fannin na kiwon dabbobi.

ADVERTISEMENT

Ya kuma yaba wa matar shugaban kasa, Sanata Oluremi Tinubu, kan ci gaba da tallafa wa matan kasar da ta ke yi.

Maiha ya kuma shaida wa mahalarta taron cewa, ba a bar matan kasar a baya ba, wajen gudunmawar da suke ci gaba da bayarwa na habaka tattalin arzikin kasar.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Ya kara da cewa, ma’aikatarsa za ta ci gaba da yin aiki kafada da kafada da aikin kungiyar ta AWARFA-N da kuma sauran abokan hadaka, domin kara samar da wata damar a fannin kiwon Zuma da kiwon Akuyoyi da samar da madarar Shanu da kuma kiwon Kajin gidan gona, musamman domin samun riba.

A nata jawabin tun da farko, Babbar Sakatariya a Ma’aikatar ta Kiwon, Chinyere Ijeoma Akujobi, ta bayyana cewa; matan kasar na ci gaba da bayar da gudunmawarsu a fannin aikin noma da samar da abinci mai gina jiki da kuma samar da kasuwar da ta dace a daukacin fadin kasar.

Ta sanar da cewa, tsarin da aka samar na kasa don kara bunkasa kiwon dabbobi, ya mayar da hankali ne ga mata da kuma matasan kasar.

A cewarta, za a kuma gudanar da taron a nan gaba; wanda a karkashin shirin bunkasa kiwo na fadar shugaban kasa, zai mayar da hankali ne ga mata da kuma matasa.

A cewarta, a karkashin shirin, za a samar da dubban ayyukan yi a kananan hukumomi 774 na kasar.

Ita kuwa, Bictoria Madedor a wajen taron, ta gabatar da aikin na kungiyar AWARFA-N na bunkasa kiwon dabbobi, har na tsawon shekaru biyar.

Ta bayyana cewa, nufin kungiyar shi ne, ci gaba da taimaka wa mata, musamman domin su zama a kan gaba wajen zuba jari da samar da sana’o’i a fannin kiwon dabbobi.

Ta kara da cewa, samar da wadatattun kudade da bunkasa fannin kiwon, domin samun riba da samar da kayan aikin kiwo na zamani, su ne mayan ginshikan da kungiyar ta mayar da hankali a kansu daga 2025 zuwa 2029.

Ita ma a sakonta na fatan alheri a wajen taron, Sarah Ossiya, wadda ta fito daga kungiyar AU-IBAR, kira ta yi da a mayar da hankali wajen kara sanya mata a cikin fannin kiwon dabbobi a kasar nan.

Ta bayyana cewa, Afirka ta yi asarar kusan kashi goma a fannin tattalin arziki, musamman wajen gaza samar da abinci mai gina jiki ga al’ummar da ke yankin, inda ta kara da cewa; samar da abinci mai gina jiki ga dabbobi, tamkar samar da shi ne ga sauran bil Adama.

Ta bukaci samar da sauye-sauye a bangaren samar da wadatattun kudade da kuma kara samar da kasar yin noma, musamman domin amfanin matan kasar da ke gudanar da kiwon dabbobi.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
DSS Ta Cafke Wanda Ya Yi Garkuwa Gami Da Kashe Wata Farfesa A 2023

DSS Ta Cafke Wanda Ya Yi Garkuwa Gami Da Kashe Wata Farfesa A 2023

LABARAI MASU NASABA

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.