ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Kudiri Aniyar Bunkasa Sana’ar Kiwon Dabbobi Ta Mata —Minista

by Leadership Hausa
8 months ago

Daga Abubakar Abba

Ministan Ma’aikatar Bunkasa Kiwon Dabbobi, Idi Mukhtar Maiha, ya sanar da cewa; gwamnatin tarayya ta sanya kudurinta, wajen bunkasa kiwon dabbobi da matan kasar ke yi.

Ya bayyana haka ne, a hirar da aka yi da shi a Abuja, inda ya ce; mata su ne kashin bayan habaka fannin tattalin arzikin kiwon dabbobi a fadin kasar.

  • NNPP Ta Rushe Shugabancinta A Kano Biyo Bayan Jita-jitar Sauya Sheƙar Abba Zuwa APC
  • Batutuwan Da Suka Ci Wa ‘Yan Adawa Tuwo A Ƙwarya A Siyasar 2025

A cewar ministan, a karkashin shirin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, gwamnatinsa ta daga darajar fannin kiwon dabbobi na kasa da kuma kara samar da dama kan sana’o’in da matan kasar ke gudanarwa, musamman domin matan su bayar da tasu gudanmawar ga fannin na kiwon dabbobi.

ADVERTISEMENT

Ya kuma yaba wa matar shugaban kasa, Sanata Oluremi Tinubu, kan ci gaba da tallafa wa matan kasar da ta ke yi.

Maiha ya kuma shaida wa mahalarta taron cewa, ba a bar matan kasar a baya ba, wajen gudunmawar da suke ci gaba da bayarwa na habaka tattalin arzikin kasar.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Ya kara da cewa, ma’aikatarsa za ta ci gaba da yin aiki kafada da kafada da aikin kungiyar ta AWARFA-N da kuma sauran abokan hadaka, domin kara samar da wata damar a fannin kiwon Zuma da kiwon Akuyoyi da samar da madarar Shanu da kuma kiwon Kajin gidan gona, musamman domin samun riba.

A nata jawabin tun da farko, Babbar Sakatariya a Ma’aikatar ta Kiwon, Chinyere Ijeoma Akujobi, ta bayyana cewa; matan kasar na ci gaba da bayar da gudunmawarsu a fannin aikin noma da samar da abinci mai gina jiki da kuma samar da kasuwar da ta dace a daukacin fadin kasar.

Ta sanar da cewa, tsarin da aka samar na kasa don kara bunkasa kiwon dabbobi, ya mayar da hankali ne ga mata da kuma matasan kasar.

A cewarta, za a kuma gudanar da taron a nan gaba; wanda a karkashin shirin bunkasa kiwo na fadar shugaban kasa, zai mayar da hankali ne ga mata da kuma matasa.

A cewarta, a karkashin shirin, za a samar da dubban ayyukan yi a kananan hukumomi 774 na kasar.

Ita kuwa, Bictoria Madedor a wajen taron, ta gabatar da aikin na kungiyar AWARFA-N na bunkasa kiwon dabbobi, har na tsawon shekaru biyar.

Ta bayyana cewa, nufin kungiyar shi ne, ci gaba da taimaka wa mata, musamman domin su zama a kan gaba wajen zuba jari da samar da sana’o’i a fannin kiwon dabbobi.

Ta kara da cewa, samar da wadatattun kudade da bunkasa fannin kiwon, domin samun riba da samar da kayan aikin kiwo na zamani, su ne mayan ginshikan da kungiyar ta mayar da hankali a kansu daga 2025 zuwa 2029.

Ita ma a sakonta na fatan alheri a wajen taron, Sarah Ossiya, wadda ta fito daga kungiyar AU-IBAR, kira ta yi da a mayar da hankali wajen kara sanya mata a cikin fannin kiwon dabbobi a kasar nan.

Ta bayyana cewa, Afirka ta yi asarar kusan kashi goma a fannin tattalin arziki, musamman wajen gaza samar da abinci mai gina jiki ga al’ummar da ke yankin, inda ta kara da cewa; samar da abinci mai gina jiki ga dabbobi, tamkar samar da shi ne ga sauran bil Adama.

Ta bukaci samar da sauye-sauye a bangaren samar da wadatattun kudade da kuma kara samar da kasar yin noma, musamman domin amfanin matan kasar da ke gudanar da kiwon dabbobi.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?
  • Leadership Hausa
    An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
DSS Ta Cafke Wanda Ya Yi Garkuwa Gami Da Kashe Wata Farfesa A 2023

DSS Ta Cafke Wanda Ya Yi Garkuwa Gami Da Kashe Wata Farfesa A 2023

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.