ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, June 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Kudiri Aniyar Bunkasa Sana’ar Kiwon Dabbobi Ta Mata —Minista

by Leadership Hausa
5 months ago

Daga Abubakar Abba

Ministan Ma’aikatar Bunkasa Kiwon Dabbobi, Idi Mukhtar Maiha, ya sanar da cewa; gwamnatin tarayya ta sanya kudurinta, wajen bunkasa kiwon dabbobi da matan kasar ke yi.

Ya bayyana haka ne, a hirar da aka yi da shi a Abuja, inda ya ce; mata su ne kashin bayan habaka fannin tattalin arzikin kiwon dabbobi a fadin kasar.

  • NNPP Ta Rushe Shugabancinta A Kano Biyo Bayan Jita-jitar Sauya Sheƙar Abba Zuwa APC
  • Batutuwan Da Suka Ci Wa ‘Yan Adawa Tuwo A Ƙwarya A Siyasar 2025

A cewar ministan, a karkashin shirin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, gwamnatinsa ta daga darajar fannin kiwon dabbobi na kasa da kuma kara samar da dama kan sana’o’in da matan kasar ke gudanarwa, musamman domin matan su bayar da tasu gudanmawar ga fannin na kiwon dabbobi.

ADVERTISEMENT

Ya kuma yaba wa matar shugaban kasa, Sanata Oluremi Tinubu, kan ci gaba da tallafa wa matan kasar da ta ke yi.

Maiha ya kuma shaida wa mahalarta taron cewa, ba a bar matan kasar a baya ba, wajen gudunmawar da suke ci gaba da bayarwa na habaka tattalin arzikin kasar.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160

Ya kara da cewa, ma’aikatarsa za ta ci gaba da yin aiki kafada da kafada da aikin kungiyar ta AWARFA-N da kuma sauran abokan hadaka, domin kara samar da wata damar a fannin kiwon Zuma da kiwon Akuyoyi da samar da madarar Shanu da kuma kiwon Kajin gidan gona, musamman domin samun riba.

A nata jawabin tun da farko, Babbar Sakatariya a Ma’aikatar ta Kiwon, Chinyere Ijeoma Akujobi, ta bayyana cewa; matan kasar na ci gaba da bayar da gudunmawarsu a fannin aikin noma da samar da abinci mai gina jiki da kuma samar da kasuwar da ta dace a daukacin fadin kasar.

Ta sanar da cewa, tsarin da aka samar na kasa don kara bunkasa kiwon dabbobi, ya mayar da hankali ne ga mata da kuma matasan kasar.

A cewarta, za a kuma gudanar da taron a nan gaba; wanda a karkashin shirin bunkasa kiwo na fadar shugaban kasa, zai mayar da hankali ne ga mata da kuma matasa.

A cewarta, a karkashin shirin, za a samar da dubban ayyukan yi a kananan hukumomi 774 na kasar.

Ita kuwa, Bictoria Madedor a wajen taron, ta gabatar da aikin na kungiyar AWARFA-N na bunkasa kiwon dabbobi, har na tsawon shekaru biyar.

Ta bayyana cewa, nufin kungiyar shi ne, ci gaba da taimaka wa mata, musamman domin su zama a kan gaba wajen zuba jari da samar da sana’o’i a fannin kiwon dabbobi.

Ta kara da cewa, samar da wadatattun kudade da bunkasa fannin kiwon, domin samun riba da samar da kayan aikin kiwo na zamani, su ne mayan ginshikan da kungiyar ta mayar da hankali a kansu daga 2025 zuwa 2029.

Ita ma a sakonta na fatan alheri a wajen taron, Sarah Ossiya, wadda ta fito daga kungiyar AU-IBAR, kira ta yi da a mayar da hankali wajen kara sanya mata a cikin fannin kiwon dabbobi a kasar nan.

Ta bayyana cewa, Afirka ta yi asarar kusan kashi goma a fannin tattalin arziki, musamman wajen gaza samar da abinci mai gina jiki ga al’ummar da ke yankin, inda ta kara da cewa; samar da abinci mai gina jiki ga dabbobi, tamkar samar da shi ne ga sauran bil Adama.

Ta bukaci samar da sauye-sauye a bangaren samar da wadatattun kudade da kuma kara samar da kasar yin noma, musamman domin amfanin matan kasar da ke gudanar da kiwon dabbobi.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
Noma Da Kiwo

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Taki Kyauta Ga Manoma 20,160

June 12, 2026
Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
Noma Da Kiwo

Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT

June 6, 2026
Next Post
DSS Ta Cafke Wanda Ya Yi Garkuwa Gami Da Kashe Wata Farfesa A 2023

DSS Ta Cafke Wanda Ya Yi Garkuwa Gami Da Kashe Wata Farfesa A 2023

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Hauhawar Farashi Ya Kai Kashi 15.93 Cikin 1000 A Watan Mayu A Nijeriya – NBS

Hauhawar Farashi Ya Kai Kashi 15.93 Cikin 1000 A Watan Mayu A Nijeriya – NBS

June 16, 2026
Sojoji Sun Ceto Matar Tsohon Kakakin Hedikwatar Tsaro A Katsina

Sojoji Sun Ceto Matar Tsohon Kakakin Hedikwatar Tsaro A Katsina

June 16, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Hukuncin Kotu Kan Ba Da Umarnin Soke Rajistar ADC

June 16, 2026
Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 8 Zuwa Sararin Samaniya

Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 8 Zuwa Sararin Samaniya

June 15, 2026
Mujallar Qiushi Za Ta Buga Muhimmin Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Ciyar Da Ilimi, Fasaha Da Kwararru Gaba Tare”

Mujallar Qiushi Za Ta Buga Muhimmin Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Ciyar Da Ilimi, Fasaha Da Kwararru Gaba Tare”

June 15, 2026
Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

June 15, 2026
Ɗan Kwankwaso Ya Zama Mataimakin Ɗan Takarar Gwamnan NDC A Zaɓen Kano na 2027

Ɗan Kwankwaso Ya Zama Mataimakin Ɗan Takarar Gwamnan NDC A Zaɓen Kano na 2027

June 15, 2026
2023: Tinubu Ya Zaɓi Kashim Shettima A Matsayin Mataimaki

Shin Har Yanzu Shettima Ne Abokin Takarar Tinubu?

June 15, 2026
Dunkulewar Kasa Shi Ne Burin Bai Daya Na Jama’ar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan

Dunkulewar Kasa Shi Ne Burin Bai Daya Na Jama’ar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan

June 15, 2026
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili

Mariya Mahmoud: Aiki A karkashin Jagorancin Wike

June 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.