ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Kudiri Aniyar Bunkasa Sana’ar Kiwon Dabbobi Ta Mata —Minista

by Leadership Hausa
5 months ago

Daga Abubakar Abba

Ministan Ma’aikatar Bunkasa Kiwon Dabbobi, Idi Mukhtar Maiha, ya sanar da cewa; gwamnatin tarayya ta sanya kudurinta, wajen bunkasa kiwon dabbobi da matan kasar ke yi.

Ya bayyana haka ne, a hirar da aka yi da shi a Abuja, inda ya ce; mata su ne kashin bayan habaka fannin tattalin arzikin kiwon dabbobi a fadin kasar.

  • NNPP Ta Rushe Shugabancinta A Kano Biyo Bayan Jita-jitar Sauya Sheƙar Abba Zuwa APC
  • Batutuwan Da Suka Ci Wa ‘Yan Adawa Tuwo A Ƙwarya A Siyasar 2025

A cewar ministan, a karkashin shirin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, gwamnatinsa ta daga darajar fannin kiwon dabbobi na kasa da kuma kara samar da dama kan sana’o’in da matan kasar ke gudanarwa, musamman domin matan su bayar da tasu gudanmawar ga fannin na kiwon dabbobi.

ADVERTISEMENT

Ya kuma yaba wa matar shugaban kasa, Sanata Oluremi Tinubu, kan ci gaba da tallafa wa matan kasar da ta ke yi.

Maiha ya kuma shaida wa mahalarta taron cewa, ba a bar matan kasar a baya ba, wajen gudunmawar da suke ci gaba da bayarwa na habaka tattalin arzikin kasar.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Ya kara da cewa, ma’aikatarsa za ta ci gaba da yin aiki kafada da kafada da aikin kungiyar ta AWARFA-N da kuma sauran abokan hadaka, domin kara samar da wata damar a fannin kiwon Zuma da kiwon Akuyoyi da samar da madarar Shanu da kuma kiwon Kajin gidan gona, musamman domin samun riba.

A nata jawabin tun da farko, Babbar Sakatariya a Ma’aikatar ta Kiwon, Chinyere Ijeoma Akujobi, ta bayyana cewa; matan kasar na ci gaba da bayar da gudunmawarsu a fannin aikin noma da samar da abinci mai gina jiki da kuma samar da kasuwar da ta dace a daukacin fadin kasar.

Ta sanar da cewa, tsarin da aka samar na kasa don kara bunkasa kiwon dabbobi, ya mayar da hankali ne ga mata da kuma matasan kasar.

A cewarta, za a kuma gudanar da taron a nan gaba; wanda a karkashin shirin bunkasa kiwo na fadar shugaban kasa, zai mayar da hankali ne ga mata da kuma matasa.

A cewarta, a karkashin shirin, za a samar da dubban ayyukan yi a kananan hukumomi 774 na kasar.

Ita kuwa, Bictoria Madedor a wajen taron, ta gabatar da aikin na kungiyar AWARFA-N na bunkasa kiwon dabbobi, har na tsawon shekaru biyar.

Ta bayyana cewa, nufin kungiyar shi ne, ci gaba da taimaka wa mata, musamman domin su zama a kan gaba wajen zuba jari da samar da sana’o’i a fannin kiwon dabbobi.

Ta kara da cewa, samar da wadatattun kudade da bunkasa fannin kiwon, domin samun riba da samar da kayan aikin kiwo na zamani, su ne mayan ginshikan da kungiyar ta mayar da hankali a kansu daga 2025 zuwa 2029.

Ita ma a sakonta na fatan alheri a wajen taron, Sarah Ossiya, wadda ta fito daga kungiyar AU-IBAR, kira ta yi da a mayar da hankali wajen kara sanya mata a cikin fannin kiwon dabbobi a kasar nan.

Ta bayyana cewa, Afirka ta yi asarar kusan kashi goma a fannin tattalin arziki, musamman wajen gaza samar da abinci mai gina jiki ga al’ummar da ke yankin, inda ta kara da cewa; samar da abinci mai gina jiki ga dabbobi, tamkar samar da shi ne ga sauran bil Adama.

Ta bukaci samar da sauye-sauye a bangaren samar da wadatattun kudade da kuma kara samar da kasar yin noma, musamman domin amfanin matan kasar da ke gudanar da kiwon dabbobi.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
DSS Ta Cafke Wanda Ya Yi Garkuwa Gami Da Kashe Wata Farfesa A 2023

DSS Ta Cafke Wanda Ya Yi Garkuwa Gami Da Kashe Wata Farfesa A 2023

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.