Dakarun rundunar Operation Haɗin Kai (OPHK) sun kashe aƙalla ’yan ta’adda 18 tare da kwato tarin makamai da harsasai a wasu hare-hare da aka kai a Jihar Borno.
Ayyukan sun gudana ne a yankunan gadar Azir na Timbuktu da kuma dajin Bulabulin, inda dakarun Sector 2 suka haɗa kai da rundunar sojin sama ta OPHK wajen kai farmaki. A cewar kakakin rundunar haɗin gwuiwa ta Arewa maso Gabas, Laftanar Kanar Sani Uba, an kashe ’yan ta’adda 11 a dajin Bulabulin, yayin da aka kashe bakwai a yankin Timbuktu.
Ya bayyana cewa dakarun sun kai sumamen a sansanonin ’yan ta’adda da ke yankunan Mar, Subdu, Yaro Lawanti da Yaro Shuwari, inda suka lalata cibiyoyin su gaba daya. A yayin farmakin, sun kuma kwato bindigogi ƙirar AK-47 guda tara, da bindigogin PKT guda uku, da babura biyar, da harsasai da kayan haɗa bama-bamai (IEDs).
Haka kuma, a wani farmaki a yankin Timbuktu, dakarun sun sake hallaka wasu ’yan ta’adda bakwai, tare da gano alamun jini da sassan jiki da ke nuna ƙarin asara a ɓangaren abokan gaba. An kuma ƙwato karin makamai da suka haɗa da bindigogi, da bututun RPG, da harsasai da na’urorin sadarwa.
Kanar Uba ya jaddada muhimmiyar rawar da rundunar sojin sama ta taka, musamman wajen samar da bayanan sirri, sa ido da kuma kai hare-haren da suka taimaka wajen samun nasarar farmakin. Ya kara da cewa ana ci gaba da gudanar da ayyukan bin sawun ’yan ta’adda domin hana su sake haduwa da kuma ƙarfafa nasarorin da aka samu.















Discussion about this post