Kungiyar Coalition for Goodluck Jonathan 2027 ta bayyana tsohon shugaban ƙasa, Goodluck Jonathan, a matsayin wanda ya fi cancanta da ƙwarewa wajen magance ƙalubalen da Nijeriya ke fuskanta, tare da tabbatar da cewa suna ƙoƙarin tsayar da shi takarar shugaban ƙasa a 2027.
Shugaban ƙungiyar, Tom Ohikere, ya bayyana hakan ne yayin wani taron manema labarai na ƙasa da ƙasa da aka gudanar a Abuja ranar Lahadi.
Ohikere ya ce ƙungiyar na tattara duk goyon baya daga faɗin Nijeriya da kuma ƙasashen waje domin dawo da Jonathan kan shugabanci. Ya ƙara da cewa ƙungiyar na aiki a matsayin cibiyar haɗin kai da ke tattaro ƙungiyoyi daban-daban da ke da burin dawo da zaman lafiya, da farfaɗo da tattalin arziƙi da kuma tabbatar da ingantaccen shugabanci.
- ‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
- Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
- Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
- ‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
- ‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano
Ya bayyana cewa Nijeriya na fama da manyan matsaloli kamar hauhawar farashi, da rashin aikin yi, da rashin tsaro da taɓarɓarewar darajar kuɗi, waɗanda suka ƙara jefa jama’a cikin wahala. A cewarsa, irin wannan yanayi na buƙatar gogaggen shugaba mai fahimtar tsarin mulki, yana mai cewa tarihin Jonathan a muƙamai daban-daban ya nuna yana da wannan ƙwarewa.
Ƙungiyar ta kuma jaddada ƙudurinta na ƙarfafa dimokuraɗiyya, gudanar da sahihin zaɓe da tabbatar da doka da oda, tare da kira ga ‘yan Nijeriya da su yi nazari kan shugabanci na baya da na yanzu domin yanke shawara mai kyau.
Ta kuma soki kalaman Atiku Abubakar da ya yi game da ƙwarewar Jonathan, tana mai cewa ba su dace da gaskiya ba, tare da jaddada cewa miƙa mulki cikin lumana da ya yi a 2015 ya kasance babban tarihi a dimokuraɗiyyar Nijeriya.














