ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwana 100 Na Mulkin Tinubu; Da Gaske Bayan Duhu Sai Haske?

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
3 years ago
Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Kwanaki 100 na farkon Gwamnatin Shugaba Bola Ahmad Tinubu, sun cika tare da yabo da kuma suka daga mabambantan bangarorin al’ummar wannan kasa.

A kwanaki 100 kacal na jaririyar gwamnatin, ta kara jefa al’ummar kasar cikin kangin fatara da talauci fiye da wanda suke ciki a gwamnatin Buhari da ta gabata, ta yadda mafi yawan jama’a ke kokawa tare da korafin cewa, sun yi zaben tumun dare dangane da gwamnatin da suka ce alkiblar da ta dosa ba mai bullewa ba ce.

  • Yadda Tinubu Ya Yi Nasara Kan Abokan Hamayyarsa Atiku Da Obi
  • Juyin Mulki: Shugaban Kasar Gabon Ya Shaki Iskar ‘Yanci Bayan Hambarar Da Gwamnatinsa

A yayin da ya karbi mulki a matsayin mutum mafi daraja ta daya a Nijeriya; a 29 ga Mayu, Shugaba Tinubu ya sha alwashin farfado da tattalin arzikin wannan kasa, wanda ya yi bahaguwar tabarbarewa a baya, lamarin da wasu ke yabawa gabanin fara gani a zahiri.

Tinubu dai na ci gaba da bai wa ‘Yan Nijeriy hakuri kan matsin da suke ciki yana mai tabbatar musu da cewa ‘bayan duhu sai haske’. Amma yaushe? wannan ita ce tambayar da galibin ‘yan kasar ke yi.

Tattalin Arziki

Masana da dama kan tattalin arziki na ganin shirye-shiryen bunkasa tattalin arziki da gwamnatin ta bullo da su suna da zaki da kuma daci a lokaci guda.

Bayanai sun nuna, sakamakon karyewar darajar naira da cire tallafin mai da aka yi sun haifar da hauhawar farashi da kashi 24.08 a watan Yulin wannan shekara. A ranar 14 ga watan Yuni, Babban Bankin Nijeriya ya umarci bankuna da su sayar da kudaden waje ba tare da wani tarnaki ba a kan farashin kasuwa. Wannan dalili ne yasa farashin naira ya yi tashin gwauron zabo, zuwa naira 915 a kan kowace dala 1 a kasuwar bayan fage.

Da yake tattaunawa da Jaridar Daily Post a makon jiya, fitaccen masani tattalin arziki, Tsohon Shugaban Kungiyar Ma’aikatan Banki, Farfesa Segun Ajibola ya bayyana cewa, an dauki matakai kwarara a watanni uku na Tinubu wadanda tsawon shekaru ake ta tsoron dauka.

“Daura damarar yaki da cin hanci da kawar da gurbatattun abubuwa a fannoni mafi tasiri na tattalin arziki a cikin kwanaki 60, ba karamin babban abin yabawa ba ne,” kamar yadda ya bayyana.

Ya ce, aikin da Shugaban Kasa ke yi tare da hadimansa da Ministoci da sauran makamantansu, hannaye ne da za a ga alfanunsu, domin a yanzu haka a kan ga kyakkyawar makomar tattalin arziki ta hanyar nada kwararru tare da ci gaba da daukar gogaggun ma’aikata, wadanda suka yi fice a cikin gwamnatinsa; domin sauke nauyi.

Sai ya ce, amma wajibi ne ‘yan Nijeriya su yi la’akari da farfadowa tare da dawowa da martabar gurbataccen tattalin arzikin Nijeriya, ba zai yiwu a dare daya ba. A cewar tasa, babban kalubalen shi ne fahimta da hadin kan dukkanin al’umma, domin a cewarsa yana da tabbacin gwamnati za ta dauki matakin da ya dace na samun nasara.

Shi ma a nasa bangaren, Babban Jami’in Gudanarwa na Kamfanin ‘SD & D Capital Management’, Idakolo Gbolade cewa ya yi, watanni uku na farko na Tinubu sun zo wa talakawa da tsauri, sai dai ya ce shirye-shiryen da aka fito da su sun samar da sabuwar rayuwa ga tattalin arziki bayan gwamnatin ta karbi mulki a mummunan yanayin rugujewar tattalin arziki.

“Kwakkwaran matakin cire tallafin man fetur da kuma kokarin daga martabar naira, duka an yi ne domin bunkasa tattalin arziki. Dakatarwa tare da binciken dakataccen Gwamnan Babban Bankin Kasa kuma, abu ne da aka yi tsammani a bisa ga illar abubuwan da ya aiwatar ga jama’a da tattalin arzikin kasa.”

Ya ce, abin da ya kamata gwamnati ta yi a gajeren zango shi ne, yin hanzarin samar da tallafin rage radadin cire tallafin mai ga al’umma tare da aiwatar da shirye-shiryen bunkasa aikin gona, tallafawa kamfanoni da sauran kananan masana’antu ta hanyar ba su bashi, domin bunkasa tattalin arziki.

A dogon zango kuwa ya ce, a zuba jari a fannin man fetur da gas, ma’adinai, makamashi da kuma aikin gona tare da kulawa ta musamman ga kananan masana’antu, domin bunkasa su. Haka zalika ya kara da cewa, gwamnatin ta dauki matakin samar da hanyar daina amfani da man fetur a zirga-zirga ta hanyar juyawa daga fetur zuwa gas, domin saukaka wa al’umma tare da baiwa matasa ayyukan yi, sai kuma daga karshe ya ce gwamnatin ta guji tsarin ciwo bashi irin na gwamnatin da ta gabata, wadda ta kai Nijeriya ga halin da take ciki yanzu.

Cire Tallafin Mai

Cire tallafin man fetur da Tinubu ya yi a jawabinsa na karbar mulki, shi ne babban abin da ya dauki hankalin jama’a tare da girgiza su, musamman bisa ga radadi da kuncin da matakin ya jefa kasa da ‘yan kasa a cikibaki-daya.

Garan Bawul A Musayar Kudade

Babban Bankin Nijeriya, ya bayar da sanarwar fitowa da sabbin ka’idoji na hada-hadar kudade, domin farfadowa da daga darajar naira. Daga cikin dokokin, akwai kafa sabuwar kasuwa ta musamman, wadda za ta rage bukatar amfani da kudaden waje.

Karin Farashin Fetur

Karin farashin man fetur da gwamnati ta yi sakamokn cire tallafin man fetur, ya kara sanya al’umma a cikin kunci da fatar. Kazalika, al’ummar kasa sun fito fili sun yi Allah- wadai da karin, kamar yadda kungiyoyin kwadago suka bukaci gwamnati ta tausayawa jama’a ta rage farashin.

Farashin man fetur din, ya tashi daga naira 195 zuwa 537 bayan cire tallafin man, sai kuma karin farashi na biyu da man ya yi zuwa 615 zuwa 650, lamarin da ya kara gurbata al’amura, rayuwa ta kara yin tsada.

Nada Shugabannin Tsaro

A ranar 19 ga watan Yuni, Shugaba Tinubu ya kori Shugabannin Hukumomi Tsaro tare da maye gurbinsu da sababbin jami’an da za su jagoranci tabbatar da tsaron kasa.

Shugabannin da suka hada da Hafsan Hafsoshi da kuma Shugaban Rundunar Sojin Kasa, Sojin Sama da Sojin Ruwa, Shugaba Tinubu ya dora musu alhakin kakkabe ayyukan ta’addanci a fadin wannan kasa baki-daya.

Dakatar Da Emefiele Tare Da Bincikensa

A ranar 9 ga watan Yuni, Shugaba Tinubu ya dakatar da Gwamnan Babban Bankin Kasa, Godwin Emefiele. Sanarwar dakatar da shi din ta bayyana cewa, an dauki matakin ne domin gudanar da bincike tare da sauya fasalin harkokin kudade da ya jagoranta a Babban Bankin Nijeriya (CBN).

Tinubun ya dauki matakin dakatar da Gwamnan Babban Bankin Kasar, wanda tsohon Shugaba Jonathan ya nada a 2014, makwanni biyu bayan karbar mulki. Tuni dai jami’an tsaron farin kaya, suka gabatar da shi a gaban kotu da tarin tuhume- tuhume 20 a shari’ar da ake ci gaba da gudanarwa, bayan janye tuhumar farko ta mallakar makamai ba bisa ka’ida ba.

Dakatar Da Shugaban EFCC

Shugaba Tinubu ya dakatar da Shugaban Hukumar Yaki da Rashawa ta EFCC, Abdurrashid Bawa a ranar 14 ga Yuni, wanda har zuwa yau yake ci gaba da zama tsare  a hannun jami’an tsaron DSS, ba tare da gurfanar da shi a gaban kotu kan laifukan da ake tuhumarsa da su ba. Tuni dai Bawa ya garzaya kotu yana kalubalantar tsare shin ba bisa ka’ida ba.

Dokar Baiwa Dalibai Bashi

A matakai na farko-farko da Gwamnatin Tarayya ta dauka  karkashin jagorancin Shugaba Tinubu shi ne, sanya hannu ga dokar baiwa daliban kasar bashi. Dokar bashin wadda ita ce irin ta ta farko a Nijeriya, bayar da rancen ya shafi daliban manyan makaratu da suka fito daga gidaje masu karamin karfi, domin su samu damar rancen karatu maras ruwa daga gidauniyar bayar da bashin karatu ta kasa.

Rushe Shugabannin Hukumomi

A wata na biyu na mulkinsa, Shugaba Tinubu ya rushe dukkanin Shugabannin Hukumomin Gwamnatin Tarayya. Hukumar Zabe ta Kasa da wasu Hukumomi 13, sun tsallake shiga cikin hukumomin da aka rushe. Tuni aka fara aikin zakulo wadanda za su maye gurbinsu.

Nada Ministoci

A kasa da kwanaki 60 na mulkinsa, Shugaba Tinubu ya tura sunayen Ministoci ga Majalisar Dattawa, domin tantance su. A kashi na farko, shugaban ya aika da sunaye 28, daga baya kuma ya sake aikawa da kashi na biyu mai dauke da sunaye 19, wadanda suka zama ‘Yan Majalisar Zartaswar Gwamnatin Tarayya 47.

Rikita- Rikitar Nijar

A sakamokn juyin mulkin da sojoji suka yi na hambarar da gwamnatin farar hula a Jamhuriyar Nijar, lamarin ya shafi Nijeriya kai tsaye. Shugaba Tinubu, wanda kuma shi ne Shugaban Kungiyar Kasashen ECOWAS, ya jagoranci taron kungiyar a inda aka cimma matsayar afkawa Nijar da yaki idan ba su mayar da mulki ga Gwamnatin Dimokuradiyya ba. Tuni dai rikita-rikitar ta Nijar ta durkusar da al’amura da dama a Nijeriya tare da zama silar karin farashin abubuwa da dama, musamman ta fuskar shigowa da abinci da sauran kayan bukatu, wanda a yanzu kuma dubban motoci ne ke tsaye dauke da kaya babu damar shiga ko fita.

Hauhawar Farashi

Ya zuwa yanzu, al’umma na cike da kunci sakamakon hauhawar farashin dukkanin abubuwan da rai ke bukata, ta yadda abubuwa da dama musamman abinci ke kokarin buwayar talaka.

Jadawalin hauhawar farashi na wannan shekara, ya karu zuwa kashi 24.08 a Yuli daga kashi 22.79 a Yuni kamar yadda ofishin kididdiga na kasa ya bayyana a tsakiyar watan Agusta. Rahoton ya nuna hauhawar farashin abincin ya tashi zuwa kashi 26.98 a Yuli daga kashi 25.25 a Yuni.

Duk da cewa, farashin abinci yana tashi sama a fadin kasa tsawon shekaru, amma yanayin a wannan lokacin ya ta’azzara ne sosai sakamakon illar shirye-shiryen gwamnati, musamman na cire tallafin man fetur da sauran makamantansu. Hukumar ta bayyana cewa, hauhawar farashin abincin shakara zuwa shekara yana faruwa ne bisa dalilin tashin farashin man fetur da sauransu.

Karuwar Talauci

Al’ummar Nijeriya da ke fama da talauci a zamanin gwamnatin da ta gabata, sun kara talaucewa kwarai da gaske a cikin kwanaki 100 na mulkin Tinubu.

Kungiyar ‘World Poberty Clock’ ta bayyana cewa akwai mutane miliyan 71 da ke fama da talauci a Nijeriya kamar yadda sakamakon kiddigar bincikensu na 2023 ya bayyana. ‘World Poberty Clock’, madubi ne da ake auna talauci a duniya. A cewar tasu mutane miliyan 133 ne matsakaitan matalauta a Nijeriya.

Tsananin talaucin da al’umma ke fama da shi a yanzu, ya sa mafi yawan jama’a kasancewa cikin kuka da kokawa da yadda mulkin Tinubu ya zo musu, wanda a baya suke fatan samun saukin al’amura bayan karewar Gwamnatin da ta gabata, amma sai ga shi talaucin da ake fama da shi a halin yanzu ya fi na baya tsanani.

Matsalar Musayar Kudade

Gagarumar matsalar harkokin musayar kudade, babban tarnaki ne ga bunkasa tattalin arzikin wannan kasa. Wasu tsare-tsare da Babban Bankin Kasa ya fito da su kan musayar kudade tare da dawowa da cibiyoyin musayar kudaden bayan dakatar da ayyukansu da gwamnatin da ta gabata ta yi, ya kara haifar da illa ga tattalin arziki ta yadda darajar naira ke ci gaba da faduwa.

Tinubu
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
+ postsBio
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Taƙaddamar Kafa Hukumar Bogi: Tinubu Ya Umarci A Yi Binciken Ƙwaƙwaf
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Shekara 200 Bayan Shehu Ɗan Fodiyo: Hubbarensa Na Ci Gaba Zama Wajen Ziyara Da Neman Tabarruki
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
Yanke Hukunci: Abubuwan Da Suka Ja Hankali A Kotun Zaben Shugaban Kasa

Yanke Hukunci: Abubuwan Da Suka Ja Hankali A Kotun Zaben Shugaban Kasa

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.