ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ma’aikatan KEDCO Sun Dakatar Da Yajin Aiki

by Abubakar Sulaiman
5 months ago
Kedco

Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Kano (KEDCO) ya sanar da dakatar da yajin aikin da ma’aikatansa suka shiga, biyo bayan cimma matsaya tsakanin shugabancin kamfanin da ƙungiyoyin ƙwadago. Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Shugaban Sadarwa na Kamfanin, Sani Bala Sani, ya sanya wa hannu.

A cewar sanarwar, an cimma wannan matsaya ne bayan “tattaunawa mai ma’ana da shawarwari na zahiri” tsakanin dukkan ɓangarorin da abin ya shafa. An bayyana cewa ƙoƙarin haɗin gwuiwa na Ƙungiyar Ƙwadago ta Ƙasa (NLC), da Hukumar BPE, da kamfanin Future Energies Africa (FEA) da Ma’aikatar Wuta da Makamashin zamani mai Ɗorewa ta Jihar Kano ne suka taimaka wajen warware matsalar.

  • KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
  • Kisan Uwa Da ‘Ya’yanta: Kotu Ta Tsare Maƙwabta 2 Kan Bayar Da Bayanan Ƙarya A Kano

KEDCO ta ce warware batutuwan da suka gada kamar bashin fansho, da albashin ma’aikata da sauran alawus-alawuswanda suke suka kasance babban abin da ta fi maida hankali a kai tun bayan shigar FEA a matsayin masu zuba jari. Kamfanin ya ƙara da cewa yana sa ran shirin da ya fara zai taimaka wajen warware waɗannan matsaloli a nan gaba.

ADVERTISEMENT

Daga cikin yarjejeniyar da aka cimma, akwai biyan bashin albashin wata na 13 (bonus) na Naira miliyan 150 da kuma bashin kuɗin tantance aiki na Naira miliyan 20 daga shekarun baya, wanda ya kai jimillar naira miliyan 170. Haka kuma, kamfanin ya yi alƙawarin biyan bashin albashin wata na 13 na shekarar 2025, wanda ya kai Naira miliyan 174, a zagayen albashin Fabrairu 2026.

Kamfanin ya kuma jaddada cewa an amince da tsarin tattaunawa mai faɗi da ta haɗa NLC, da ƙungiyoyin ma’aikatan wutar lantarki da kwamitin daraktocin KEDCO domin magance sauran matsaloli. Sanarwar ta ƙare da cewa an dawo da ayyuka kamar yadda aka saba a dukkan yankunan da kamfanin ke yin aiki, tare da tabbatar wa abokan hulɗa da al’umma cewa za a ci gaba da inganta samar da wutar lantarki da kyautata hulɗar aiki.

LABARAI MASU NASABA

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Kedco
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
  • Abubakar Sulaiman
    Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
  • Abubakar Sulaiman
    Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka
  • Abubakar Sulaiman
    Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

MASU ALAKA

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi
Manyan Labarai

Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

June 13, 2026
Next Post
Tsofaffin Manyan Sakatarori Sun Karrama Gwamna Lawal, Sun Yaba Da Ayyukan Ci Gaban Zamfara

Tsofaffin Manyan Sakatarori Sun Karrama Gwamna Lawal, Sun Yaba Da Ayyukan Ci Gaban Zamfara

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.