ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ma’aikatan KEDCO Sun Dakatar Da Yajin Aiki

by Abubakar Sulaiman
8 months ago
Kedco

Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Kano (KEDCO) ya sanar da dakatar da yajin aikin da ma’aikatansa suka shiga, biyo bayan cimma matsaya tsakanin shugabancin kamfanin da ƙungiyoyin ƙwadago. Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Shugaban Sadarwa na Kamfanin, Sani Bala Sani, ya sanya wa hannu.

A cewar sanarwar, an cimma wannan matsaya ne bayan “tattaunawa mai ma’ana da shawarwari na zahiri” tsakanin dukkan ɓangarorin da abin ya shafa. An bayyana cewa ƙoƙarin haɗin gwuiwa na Ƙungiyar Ƙwadago ta Ƙasa (NLC), da Hukumar BPE, da kamfanin Future Energies Africa (FEA) da Ma’aikatar Wuta da Makamashin zamani mai Ɗorewa ta Jihar Kano ne suka taimaka wajen warware matsalar.

  • KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
  • Kisan Uwa Da ‘Ya’yanta: Kotu Ta Tsare Maƙwabta 2 Kan Bayar Da Bayanan Ƙarya A Kano

KEDCO ta ce warware batutuwan da suka gada kamar bashin fansho, da albashin ma’aikata da sauran alawus-alawuswanda suke suka kasance babban abin da ta fi maida hankali a kai tun bayan shigar FEA a matsayin masu zuba jari. Kamfanin ya ƙara da cewa yana sa ran shirin da ya fara zai taimaka wajen warware waɗannan matsaloli a nan gaba.

ADVERTISEMENT

Daga cikin yarjejeniyar da aka cimma, akwai biyan bashin albashin wata na 13 (bonus) na Naira miliyan 150 da kuma bashin kuɗin tantance aiki na Naira miliyan 20 daga shekarun baya, wanda ya kai jimillar naira miliyan 170. Haka kuma, kamfanin ya yi alƙawarin biyan bashin albashin wata na 13 na shekarar 2025, wanda ya kai Naira miliyan 174, a zagayen albashin Fabrairu 2026.

Kamfanin ya kuma jaddada cewa an amince da tsarin tattaunawa mai faɗi da ta haɗa NLC, da ƙungiyoyin ma’aikatan wutar lantarki da kwamitin daraktocin KEDCO domin magance sauran matsaloli. Sanarwar ta ƙare da cewa an dawo da ayyuka kamar yadda aka saba a dukkan yankunan da kamfanin ke yin aiki, tare da tabbatar wa abokan hulɗa da al’umma cewa za a ci gaba da inganta samar da wutar lantarki da kyautata hulɗar aiki.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Kedco
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Sokoto, Sun Kashe Mutane 7, Sun Yi Garkuwa Da 12

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Tsofaffin Manyan Sakatarori Sun Karrama Gwamna Lawal, Sun Yaba Da Ayyukan Ci Gaban Zamfara

Tsofaffin Manyan Sakatarori Sun Karrama Gwamna Lawal, Sun Yaba Da Ayyukan Ci Gaban Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.