Majalisar dokokin jihar Kano ta tabbatar da Murtala Sule Garo a matsayin sabon mataimakin gwamnan jihar, bayan kammala tantance shi cikin nasara.
Tabbatarwar ta biyo bayan amincewa da rahoton kwamitin wucin gadi da majalisar ta kafa, a zaman da Kakakin majalisar, Jibril Isma’il Falgore ya jagoranta.
Shugaban kwamitin kuma Mataimakin Kakaki, Muhammad Bello, ya bayyana cewa naɗin Garo ya biyo bayan murabus ɗin tsohon mataimakin gwamna, Aminu Abdussalam Gwarzo. Ya ƙara da cewa an yi cikakken tantancewa, ciki har da tambayoyi kan ilimi, ƙwarewa, da hangen nesansa kan shugabanci.
Kwamitin ya ce Garo ya nuna fahimta mai kyau kan nauyin ofishin da kuma yadda zai tallafa wa gwamna Abba Kabir Yusuf wajen aiwatar da manufofin gwamnati.
Bayan amincewa da rahoton, Kakakin majalisar ya gabatar da batun ga zauren majalisa, inda ‘yan majalisa suka amince gaba ɗaya da naɗin, wanda ya tabbatar da Garo a hukumance a matsayin mataimakin gwamnan Kano.















Discussion about this post