Ƙungiyar Malaman Nijeriya reshen FCT, (Nigeria Union of Teachers (NUT), ta dakatar da yajin aikin da take yi nan take bayan samun sabbin alƙawurra daga Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, na magance matsalolin malamai.
Matakin ya fito ne a cikin wata sanarwa bayan taron gaggawa na majalisar gudanarwa ta ƙungiyar (SWEC) da aka gudanar a Gwagwalada ranar Lahadi. Tun da farko, malaman sun shiga yajin aiki ne tun ranar 20 ga Afrilu, 2026, sakamakon buƙatun da suka haɗa da biyan haƙƙokinsu da kuma duba batun ƙarin girma.
A cewar ƙungiyar, ministan ya amince da ware Naira biliyan 5 duk wata domin biyan alawus-alawus da sauran basussuka, inda N2bn za su fito daga kuɗaɗen shiga na FCT, yayin da N3bn za su fito daga kaso na kuɗaɗen shiga na ƙananan hukumomi. Haka kuma, ya yi alƙawarin warware matsalar ƙarin girma bayan ganawa da hukumar kula da ma’aikata.
Bayan tattaunawa mai zurfi, ƙungiyar ta umarci dukkan malamai su koma bakin aiki daga Litinin, 27 ga Afrilu, 2026, tana mai gargaɗin cewa za ta sake duba matsayinta idan ba a cika alƙawurran da aka ɗauka ba, tare da tabbatar da cewa babu wanda za a hukunta saboda shiga yajin aikin.















Discussion about this post