Masu ruwa da tsaki a fannin noma sun yi kira da a ƙara zuba jari a binciken noma tare da ba ƙananan manoma muhimmanci, domin inganta tsaron abinci a Nijeriya. Sun bayyana hakan ne a taron shekara-shekara na Cibiyar Binciken Noma (IAR), inda aka tattauna hanyoyin ƙarfafa samar da abinci a cikin gida.
Daraktan cibiyar ya jaddada muhimmancin dogaro da abin da ake nomawa a cikin ƙasa, yana mai cewa ƙananan manoma su ne ginshiƙin tsarin noma na ƙasa. Ya kuma buƙaci gwamnati da masu zaman kansu da su ƙara saka jari a bincike da sabbin fasahohin noma domin ƙara yawan amfanin gona.
Ya bayyana cewa cibiyar ta fara amfani da hanyoyin dijital wajen isar da sakamakon bincike ga manoma, duk da cewa ƙarancin kuɗi na ci gaba da zama babban ƙalubale ga aikin bincike da bunƙasa noma.

Da yake buɗe taron, Mataimakin Shugaban Jami’ar Ahmadu Bello (ABU) ya yaba da haɗin gwuiwar da ke tsakanin jami’ar da cibiyar, yana mai cewa zai iya zama abin koyi ga sauran cibiyoyi. Ya kuma ƙarfafa a ƙara haɗa kai tsakanin masu bincike da manoma.
A ƙarshe, an bayyana cewa taron zai taimaka wajen ƙarfafa tattaunawa da samar da sabbin tsare-tsare da za su inganta tsaron abinci da bunƙasa tattalin arziƙi ta hanyar noma mai ɗorewa.















Discussion about this post