ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NPA Ta Kara Kaimi Wajen Lalubo Da Mafita Kan Kalubale A Tashsohin Jiragen

by Bello Hamza and Sulaiman
5 months ago
NPA

Shugaban Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA, Dakta Abubakar Dantsoho, ya bayyana cewa, Hukumar ta yi hadaka da Hukumar kasa da kasa da ke lura da bangaren zirga-zirgar Jiragen Ruwa IMO.

Dantsoho ya sanar da cewa, hukomin biyu, sun hadakar ce, bisa nufin samar da tsarin PCS, wanda zai taimaka, wajen magance masatalar da ake fuskanta, na gudanar da ayyukan da ake gudanarwa, a Tashoshin Jiragen Ruwa na kasar

  • Gwamna Lawal Ya Lashe Kyautar Gwarzon Gwamnan Shekara Ta Jaridar LEADERSHIP
  • Rahoton Tsaro Na Munich Ya Nuna Tsamin Dangantaka Tsakanin Amurka Da Turai

Shugaban ya bayyana haka ne, a taron bita na kwana uku da manyan masu ruwa da tsaki, da aka gudanar a jihar Legas.

ADVERTISEMENT

Shirin bunkasa yanayin kasuwanci, na Fadar Shugaban Kasa ne, ya shirya taron wato PEBEC da NPA ne, suka shirya taron.

Kazalika, manufar hada taron, ya hada da, kara inganta samar da sauki na gudanar da hada-hadar kasuwanci.

LABARAI MASU NASABA

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

A cewar shugaban hukumar na NPA, tsarin na PCS, zai kuma taimaka wa, tsarin kasa da Hukumar ta bullo da shi, wato NSW.

Ya kara da cewa, tsarin zai kuma taimaka, wajen samun bayani ga masu ruwa da tsaki tare da rage jinkirin da ake samu a baya, na adana bayanai a cikin kundin gudanar da ayyuka, a Tashoshin Jiragen Ruwan kasar.

A na ta jawabin, Darakta Janar ta PEBEC, Madam Zahrah Mustapha, ta bayyana cewa, hadakar ta wuce batun gano matsalolin, har kuma mayar da hankali, kan wanzar da tsarin, wanda tuni, ya kamata ace, an fara lalubo da mafita.

“Nijeriya dai, a kullum, na tabka babbar asara saboda rashin samun nasarar gudanar da ayyuka,” Inji Madam Zahrah.

“Wannan ba wai kawai batu ne, na alkaluma, abu ne da yake a zahirance na rasa gudanar da ayyuka da kuma rashin kirkiro da wasu ayyukan yi, inda hakan ke kawo tsako, a fannin kara bunkasa tattalin arzikin kasar,” A cewarta.

Ta kara da cewa, wannan sauyin da aka kawo, zai kara taimaka wa, wajen kara habaka albarkatun da ke a fannin tattalin arzikin kasar.

Ta ci gaba da cewa, tsarin zai kuma janyo hukumomin gwamnati da ke sanya ido a fannin Tashoshin Jiragen Ruwan kasar da masu ruwa da tsaki da kamfaonin, masu zaman kansu, domin a tabbatar da ana bin ka’ida wajen gudanar da ayyuka, musamman bisa nufin rage cunkoso a wajen da ake ajiya Jiragen Ruwa a Tashoshin Jiragen Ruwan kasar.

Idan za a iya tunawa, a 2025, Hukumar NPA ta samu gagarumar nasarar da ta kai kaso 100, bisa sauye-sauyen da ta samu, ta hanyar PEBEC, wanda hakan ya sanya, ta kai mataki na biyar, a tsakanin sauran hukumomin gwamnati da kaso 84.2 na bin ka’ida.

Kazalika, sakamakon da ya fito daga gun masu ruwa da tsaki kan wannan hadakar, ana sa ran, za a fara wanzar da shi, a watanni masu zuwa.

Idan aka cike gibin da aka gano a yayin zagayen aikin sanya ido, Hukumar ta NPA da kuma PEBEC, na da nufin kara habaka wanzar da sabuwar gasa, a fannin na sufurin Jiragen Ruwa da samar da kyakyawan yanayi, wanda hakan, zai bayar da damar, janyo masu hannun jari, a fannin da kuma kara samar da damar, gudanar da hada-hadar kasuwanci.

NPA
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba
NPA
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tattalin Arziki

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

July 11, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Tattalin Arziki

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani
Tattalin Arziki

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
Next Post
Babu Hannun Ganduje A Sace Dadiyata – Shehu Sani

Babu Hannun Ganduje A Sace Dadiyata - Shehu Sani

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.