Shugaban Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA, Dakta Abubakar Dantsoho, ya bayyana cewa, Hukumar ta yi hadaka da Hukumar kasa da kasa da ke lura da bangaren zirga-zirgar Jiragen Ruwa IMO.
Dantsoho ya sanar da cewa, hukomin biyu, sun hadakar ce, bisa nufin samar da tsarin PCS, wanda zai taimaka, wajen magance masatalar da ake fuskanta, na gudanar da ayyukan da ake gudanarwa, a Tashoshin Jiragen Ruwa na kasar
- Gwamna Lawal Ya Lashe Kyautar Gwarzon Gwamnan Shekara Ta Jaridar LEADERSHIP
- Rahoton Tsaro Na Munich Ya Nuna Tsamin Dangantaka Tsakanin Amurka Da Turai
Shugaban ya bayyana haka ne, a taron bita na kwana uku da manyan masu ruwa da tsaki, da aka gudanar a jihar Legas.
Shirin bunkasa yanayin kasuwanci, na Fadar Shugaban Kasa ne, ya shirya taron wato PEBEC da NPA ne, suka shirya taron.
Kazalika, manufar hada taron, ya hada da, kara inganta samar da sauki na gudanar da hada-hadar kasuwanci.
A cewar shugaban hukumar na NPA, tsarin na PCS, zai kuma taimaka wa, tsarin kasa da Hukumar ta bullo da shi, wato NSW.
Ya kara da cewa, tsarin zai kuma taimaka, wajen samun bayani ga masu ruwa da tsaki tare da rage jinkirin da ake samu a baya, na adana bayanai a cikin kundin gudanar da ayyuka, a Tashoshin Jiragen Ruwan kasar.
A na ta jawabin, Darakta Janar ta PEBEC, Madam Zahrah Mustapha, ta bayyana cewa, hadakar ta wuce batun gano matsalolin, har kuma mayar da hankali, kan wanzar da tsarin, wanda tuni, ya kamata ace, an fara lalubo da mafita.
“Nijeriya dai, a kullum, na tabka babbar asara saboda rashin samun nasarar gudanar da ayyuka,” Inji Madam Zahrah.
“Wannan ba wai kawai batu ne, na alkaluma, abu ne da yake a zahirance na rasa gudanar da ayyuka da kuma rashin kirkiro da wasu ayyukan yi, inda hakan ke kawo tsako, a fannin kara bunkasa tattalin arzikin kasar,” A cewarta.
Ta kara da cewa, wannan sauyin da aka kawo, zai kara taimaka wa, wajen kara habaka albarkatun da ke a fannin tattalin arzikin kasar.
Ta ci gaba da cewa, tsarin zai kuma janyo hukumomin gwamnati da ke sanya ido a fannin Tashoshin Jiragen Ruwan kasar da masu ruwa da tsaki da kamfaonin, masu zaman kansu, domin a tabbatar da ana bin ka’ida wajen gudanar da ayyuka, musamman bisa nufin rage cunkoso a wajen da ake ajiya Jiragen Ruwa a Tashoshin Jiragen Ruwan kasar.
Idan za a iya tunawa, a 2025, Hukumar NPA ta samu gagarumar nasarar da ta kai kaso 100, bisa sauye-sauyen da ta samu, ta hanyar PEBEC, wanda hakan ya sanya, ta kai mataki na biyar, a tsakanin sauran hukumomin gwamnati da kaso 84.2 na bin ka’ida.
Kazalika, sakamakon da ya fito daga gun masu ruwa da tsaki kan wannan hadakar, ana sa ran, za a fara wanzar da shi, a watanni masu zuwa.
Idan aka cike gibin da aka gano a yayin zagayen aikin sanya ido, Hukumar ta NPA da kuma PEBEC, na da nufin kara habaka wanzar da sabuwar gasa, a fannin na sufurin Jiragen Ruwa da samar da kyakyawan yanayi, wanda hakan, zai bayar da damar, janyo masu hannun jari, a fannin da kuma kara samar da damar, gudanar da hada-hadar kasuwanci.















Discussion about this post