Tsohon sanatan Adamawa, Ishaku Abbo, ya musanta rahotannin da ke alaƙanta shi da jam’iyyar NDC, yana mai cewa ba mamba ba ne shi, yayin da yake shirin ficewa daga jam’iyyar ADC sakamakon rikicin da ke ƙara tsananta a jihar Adamawa. Ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook ranar Laraba, inda ya yi jawabi ga magoya bayansa.
Abbo ya ce da dama daga cikin magoya bayansa sun shiga ADC ne domin tallafa masa, amma ya yi gargaɗin cewa tsarin jam’iyyar a Adamawa na iya kawo cikas ga damar su a zaɓen 2027. Ya zargi jam’iyyar da gudanar da tarukan mazaɓu ba tare da bin umarnin kotu guda biyu da aka bayar ba, lamarin da ya haifar da abin da ya kira shugabannin jiha marasa da ba halattattu ba.
Ya ƙara da cewa duk wani zaɓen fidda gwani da za a gudanar ƙarƙashin irin wannan shugabanci ba zai samu iko a doka ba, kuma kotu na iya soke shi. Ya yi nuni da abin da ya faru a shari’ar PDP ta Filato a 2023, inda aka kwace kujeru daga ‘yan takarar jam’iyyar saboda saɓa umarnin kotu, wanda ya anfani ‘yan takarar APC da suka zo na biyu.
Abbo ya ce dokar zaɓe ta bai wa ‘yan siyasa damar sauya jam’iyya har zuwa ranar 10 ga Mayu, 2026, yana mai kira ga magoya bayansa da su kwantar da hankalinsu yayin da ake kammala shirye-shiryen neman sabuwar jam’iyya.
Ya kuma bayyana cewa zai sanar da matsayinsa nan da ƙarshen mako, yana mai cewa shi da magoya bayansa za su fito da sabuwar hanyar siyasa yayin da rikicin ADC a Adamawa ke ci gaba da zurfafa.














Discussion about this post