ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Obasanjo Ya Buƙaci A Kawo Ƙarshen Cin Zarafin Yara Ƙanana

by Rabi'u Ali Indabawa
4 months ago
Obasanjo

A ranar Litinin ce Tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo, ya yi kira da a ƙara kulawa da yara, yana mai bayyana su a matsayin ginshiƙin makomar kowace al’umma.

Obasanjo ya yi wannan kiran ne yayin da yake karvar baƙuncin shugabannin Ƙungiyar Likitocin Yara ta Nijeriya, ƙarƙashin jagorancin shugabarta, Dakta Ekanem Ekure, a gidansa da ke cikin Olusegun Obasanjo Presidential Library a Abeokuta.

  • Rikicin Boko Haram Ya Daɗe Fiye da Yaƙin Basasar Najeriya – Obasanjo
  • Gasar Euro 2024: Yadda Kasashe Suka Gayyaci ‘Yan Wasa

Tsohon shugaban ƙasar ya ce likitocin yara na taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da lafiyar yara, don haka bai kamata su gaji ba wajen ƙara ɗaga matsayin ƙwarewa da kuma yin ƙoƙari fiye da da wajen kula da yara, waɗanda ya bayyana a matsayin fata da makomar kowace al’umma.

ADVERTISEMENT

Obasanjo ya ce ko da yake ya daina haihuwa, wasu daga cikin ’ya’yansa ma sun daina haihuwa, amma jikokinsa suna ci gaba da haihuwa, yana mai jaddada muhimmanci da matsayin yara wajen ci gaba da wanzuwar al’umma da zuri’a.

Tsohon shugaban ƙasar ya ce saboda wannan muhimmanci na samun yara masu ƙoshin lafiya a cikin al’umma, zai amince da rawar ba da shawara da ƙungiyar ta ɗora masa, yana mai cewa zai ci gaba da tallafa wa duk wani yunƙuri da ke nufin inganta walwalar yara a faɗin duniya.

LABARAI MASU NASABA

Shekara 3 Da Shirin Ceto Jihar Zamfara: Jinjina Ta Musamman Ga Gwamna Dauda Lawal

Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi

Obasanjo ya ce, “A matsayinku na ƙwararru a fannin kula da lafiyar yara, aikinku aiki ne na rai da mutuwa. A matsayinku na likitan yara, kuna da wata ƙwarewa ta musamman domin kuna hulɗa da yara.

“Kuma matsalar kula da yara ita ce ba su kama da manya; dole ne ku iya jin tausayinsu. Idan ni ne manya na zo wurinku, za ku tambaye ni inda nake jin ciwo, ko a dama ko a hagu, yadda nake ji da dare, amma yara ba za su iya faɗin duk waɗannan ba.

“Saboda haka fannin ƙwarewarku na da matuƙar muhimmanci. Don haka aikin da kuka ba ni na zama mai kare haƙƙin yara, zan karve shi da hannu bibbiyu.

“Ba zan ƙara haihuwa ba, domin ’ya’yana sun manyanta, amma ’ya’yana suna haihuwa, jikokina ma suna haihuwa, don haka ba zan tava daina samun yara ba.

“Domin idan na daina, ’ya’yana ba za su daina ba, idan ’ya’yana sun daina, jikokina ba za su daina ba, kuma zagayowar rayuwa tana ci gaba. Saboda haka ina ƙarfafa ku da ku ci gaba da yin iyakar ƙoƙarinku wajen ba da kulawa mafi kyau ga ƴa’yanmu, domin su ne ainihin makomarmu.”

A baya, Ekure ta yaba wa tsohon shugaban ƙasar, tana mai bayyana shi a matsayin fitaccen jigo na duniya da shugaba mai jajircewa wajen inganta walwala da jin daɗin jama’a a faɗin duniya.

Ta ce ƙungiyar ta zo Abeokuta ne domin gudanar da Babban Taron Shekara-shekara na 57 da Taron Kimiyya, kuma tana so tsohon shugaban ƙasar ya zama mai kare walwalar yara.

Ekure ta ce, “Mun zo ne domin roƙonku da ku zama mai kare haƙƙin yaran Nijeriya. Fiye da rabin ’yan Nijeriya yara ne da matasa, kuma su babbar dukiya ce ga ƙasar.

“Abin takaici, waɗannan na fama da cututtukan da za a iya hana su, take haƙƙin bil’adama da walwalarsu, da kuma rashin gina jiki, wanda ke da matuƙar tayar da hankali.

“Shi ya sa muka zo wurinka, domin mun san kana da matsayi na musamman a matsayinka na tsohon shugaban ƙasa dattijo mai daraja, wanda hakan ke sa muryarku ta yi ƙarfi kuma ta yi tasiri.

“Duk abin da kuka faɗa, gwamnati da jama’a za su saurara,” in ji ta.

Da take magana da manema labarai gabanin Babban Taron Shekara-shekara na 57 da Taron Kimiyya na ƙungiyar, Ekure ta bayyana cewa fiye da jarirai 800 na mutuwa a kowace rana, duk da cewa mafi yawancin mutuwar ana iya shawo kanta.

Obasanjo
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

An Cafke Motocin Dako 50 Makare Da Abinci Za Su Shiga Nijar A Zamfara
Labarai

Shekara 3 Da Shirin Ceto Jihar Zamfara: Jinjina Ta Musamman Ga Gwamna Dauda Lawal

June 5, 2026
Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
Tsaro

Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi

June 5, 2026
An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe
Labarai

An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe

June 5, 2026
Next Post
Jihar Gombe Ta Kafa Kwamitin Sasanta Rikicin Manoma Da Makiyaya

Jihar Gombe Ta Kafa Kwamitin Sasanta Rikicin Manoma Da Makiyaya

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin: Za a Gudanar Da Bukukuwa Fiye Da 100 Na “Fitar Da Kayayyaki Zuwa Kasar Sin” a Shekara Ta 2026

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin: Za a Gudanar Da Bukukuwa Fiye Da 100 Na “Fitar Da Kayayyaki Zuwa Kasar Sin” a Shekara Ta 2026

June 5, 2026
Xi Jinping Zai Kai Ziyarar Aiki A DPRK

Xi Jinping Zai Kai Ziyarar Aiki A DPRK

June 5, 2026
Bukatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

Bukatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

June 5, 2026
‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa

‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa

June 5, 2026
An Cafke Motocin Dako 50 Makare Da Abinci Za Su Shiga Nijar A Zamfara

Shekara 3 Da Shirin Ceto Jihar Zamfara: Jinjina Ta Musamman Ga Gwamna Dauda Lawal

June 5, 2026
Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi

Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi

June 5, 2026
An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe

An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe

June 5, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Ma’aurata A Abuja

Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Ma’aurata A Abuja

June 5, 2026
Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi

Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi

June 5, 2026
An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

June 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.