Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa kiran da ake yi na ganin an dawo da tsarin biyan tallafin man fetur yana nuna “tsantsar rashin sanin makamar mulki da kuma rashin sanin tattalin arziƙi.” Shugaban ya jaddada cewa tsarin tallafin da aka yi a baya ya jefa jihohi cikin mummunan mawuyacin halin ƙuncin tattalin arziƙi.
Tinubu ya bayyana hakan ne a lokacin da ya karɓi baƙuncin Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke a fadar shugaban kasa jim kaɗan bayan ziyarar gwamnan a Abuja. Ya ce ya ga bayanin ɗaya daga cikin abokan hamayyarsa na siyasa, (Atiku Abubakar, wanda ya ce zai dawo da tallafin man fetur idan an zaɓe shi a 2027), inda shugaban ya ce wannan wani yunƙuri ne kawai don yaudara, sakamakon irin halin ƙaƙani-kayi da jihohi suka shiga a baya gabanin hawansa mulki.
Shugaba Tinubu ya tuna yadda kafin zuwansa, jihohi 27 suka gaza biyan albashin ma’aikatansu da ‘yan fansho sakamakon tsarin biyan tallafin mai wanda ya yi wa gwamnati katutu. Ya kuma yi nuni da halin da jihar Osun ta tsinci kanta a ciki a wancan lokacin inda aka yi wa wani da ya sani laƙabi da “Gwamnan rabin albashi.”
Daga ƙarshe, shugaban ƙasar ya ƙara da cewa nauyi ne da ya rataya a wuyan gwamnati a dukkan matakai ta samar da muhimman ababen more rayuwa ga ‘yan Nijeriya maimakon bayar da kuɗin ta wata hanyar da ba ta dace ba. Ya yi kira ga Gwamna Adeleke da ya tabbatar ya yi amfani da damar da al’ummar jihar Osun suka sake ba shi don gina ƙasa da ciyar da dimokuraɗiyya gaba.














