ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Wike Da Fubara Na Ƙara Tsananta, Tinubu Ya Sake Shiga Tsakani

by Abubakar Sulaiman
6 months ago
Fubara

LABARAI MASU NASABA

Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sake tsoma baki a rikicin siyasa da ke ci gaba da gudana tsakanin Gwamnan Jihar Ribas Siminalayi Fubara, da Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike. Majiyoyi masu tushe sun bayyana cewa Tinubu ya gayyaci Wike zuwa wani muhimmin taro a ƙasashen waje domin shawo kan sabon rikicin da ya sake ɓarkewa a a jihar mai arzikin man fetur.

Rahotanni sun nuna cewa ana sa ran taron zai gudana ne a birnin Dubai na ƙasar Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE), bayan Shugaban Ƙasa ya kammala wata gajeriyar ziyarar aiki a Faransa. Wata majiya daga fadar shugaban ƙasa ta ce Tinubu na kallon matakan da Wike ke ɗauka a matsayin barazana ga zaman lafiya a yankin Neja-Delta, tare da jaddada cewa ba za a amince da duk wani yunƙurin tsige Gwamna Fubara ba.

  • Sakataren APC Ya Buƙaci Murabus Ɗin Wike Saboda “Tsoma Baki” A Harkokin Jam’iyya
  • Jam’iyyar APC Ta Ribas Ta Yi Watsi Da Matakin Tsige Gwamna Fubara

Rikicin ya ƙara tsananta ne bayan ƴan majalisar dokokin Jihar Rivers 27, waɗanda ake ganin suna goyon bayan Wike, suka ƙaddamar da sabon yunƙurin tsige Gwamna Fubara da mataimakiyarsa, Farfesa Ngozi Odu. An zargi gwamnan da manyan laifuka kamar rusa ginin majalisa, da kashe kuɗaɗe ba tare da kasafi ba, da kuma bijirewa hukuncin Kotun Ƙoli kan ikon kuɗaɗen majalisa, yayin da aka zargi mataimakiyar gwamnan da almubazzaranci da toshe ayyukan majalisa.

ADVERTISEMENT

Duk da ƙoƙarin sasanci da Tinubu ya yi a baya, zaman lafiyar da aka samu na wucin gadi ya rushe bayan watanni kaɗan. Rikicin ya sake ɗaukar sabon salo da zargin cin amana da kalaman siyasa masu zafi, lamarin da ya jawo kira daga manyan ‘yan siyasa da jam’iyyar APC na ƙasa da ƙasa da a sake sasantawa domin kare zaman lafiya, da tsaro da martabar Shugaban Ƙasa, tare da hana rikicin haifar da tangarɗa ga tattalin arziƙi da tsaron ƙasa.

Fubara
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah
  • Abubakar Sulaiman
    Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu
  • Abubakar Sulaiman
    Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano
  • Abubakar Sulaiman
    An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

MASU ALAKA

Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah
Manyan Labarai

Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

July 18, 2026
Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Next Post
Kuskure Ne Daukar Harkar Fim A Matsayin Sana’a Kadai —Maryam CTV (2)

Kuskure Ne Daukar Harkar Fim A Matsayin Sana’a Kadai —Maryam CTV (2)

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

July 18, 2026
Tasirin Da VAR Ta Yi A Gasar Kofin Duniya

Tasirin Da VAR Ta Yi A Gasar Kofin Duniya

July 18, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.