Mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da wasu shida suka jikkata sakamakon rikicin da ya ɓarke tsakanin manoma da makiyaya a ƙauyukan Lanzai da Dosho da ke ƙaramar hukumar Darazo a jihar Bauchi. Rikicin ya kuma haddasa asarar dukiyoyi da dama, ciki har da ƙone gidaje da rugage.
Kakakin rundunar ’yansandan jihar Bauchi, SP Nafiu Habib, ya ce lamarin ya fara ne bayan wasu da ake zargin makiyaya ne sun kai hari kan manoma da ke zuba taki a gonakinsu a wajen ƙauyen Lanzai. Daga baya, wasu matasa daga ƙauyen suka kai harin ramuwar gayya zuwa Dosho, inda suka banka wa wasu sassan ƙauyen wuta.
A cewarsa, kimanin ruga 50 ne suka ƙone ƙurmus tare da lalacewar dukiyoyi masu yawa. Rundunar ta ce ta tura jami’an tsaro na musamman da kuma na sashin yaƙi da manyan laifuka (VCRU) domin dawo da zaman lafiya da hana rikicin yaɗuwa zuwa sauran ƙauyukan da ke maƙwabtaka da yankin.
Kwamishinan ’yansandan jihar, CP Sani-Omolori Aliyu, ya ba da umarnin gudanar da cikakken bincike kan lamarin tare da tabbatar da gurfanar da duk wanda aka samu da hannu a rikicin. Ya kuma yi kira ga mazauna yankunan da su kwantar da hankalinsu tare da kauce wa ɗaukar doka a hannunsu.















Discussion about this post