ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabuwar Shekara: Sanata Danbaba Ya Taya ‘Yan Nijeriya Murna, Ya Yaba Da Jagorancin Tinubu

by Leadership Hausa
7 months ago

Daga Rabi’u Ali Indabawa

Sanata mai wakiltar Mazaɓar Sakkwato ta Kudu a Majalisar Dattawa ta 8 da ta 9, Ibrahim Abdullahi Danbaba Dambuwa (DBB), ya bayyana cewa, shugaba Bola Tinubu ya kudiri aniyar magance dukkan kalubalen da kasar nan ke ciki. Sanata Danbaba ya bayyana haka a cikin sakonsa na taya ‘yan Nijeriya murnar shiga sabuwar shekarar 2026, tare da addu’ar fatan alheri.

 

ADVERTISEMENT

“Yayin da muka shiga sabuwar shekarar 2026, ina mika gaisuwa ta musamman da fatan alheri ga daukacin al’ummar Jihar Sakkwato da kuma ‘yan Nijeriya baki daya. Allah ya sanya wannan shekara ta zama ta sabuwar fata, zaman lafiya da ci gaba mai dorewa ga kasarmu mai albarka,” in ji shi.

  • ’Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Sace Matan Aure A Kaduna
  • Da Ɗumi-Ɗumi: Chelsea Ta Raba Gari Da Koci Enzo Maresca

Ya ce, “Ina amfani da wannan dama domin taya ‘yan Nijeriya murna da kuma mika gaisuwa ta musamman ga Mai Girma Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, jagora mai jarumta da kishin kasa wanda jajircewarsa wajen sauya fasalin Nijeriya ke kara zaburar da miliyoyin ‘yan kasa.

LABARAI MASU NASABA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

 

“Gwamnatin Shugaban Kasa Bola Tinubu ta dauki matakai masu karfi na gyara, duk da kalubale da suka biyo baya, kuma suna gina tubalin sabuwar Njjeriya mai karfi da dogaro da kanta.

 

“Kokarinka a matsayin Shugaban Kasa na farfado da tattalin arziki, karfafa hukumomi da inganta tsaro abin yabo ne. Saboda haka, ina kira ga yan Nijeriya da su ci gaba da nuna hakuri da goyon baya domin ganin wadannan manufofi sun haifar da gagarumin sakamako a nan gaba,” in ji shi.

 

Ya c igaba da cewa; “Ga Mai Girma Gwamnan Jihar Sakkwato, Dr. Ahmed Aliyu (PhD, FCNA, ACIT), ina mika godiya ta musamman bisa jajircewarka wajen ci gaban jiharmu.

 

Ayyukanka a fannonin gine gine, kiwon lafiya, ilimi da tsaro sun nuna hangen nesan ka na gina Sakkwato daya, mai ci gaba da hadin kai. Jagorancinka ya dawo da kuzari a harkokin mulki tare da farfado da fatan al’umma.

 

Haka zalika, ina mika girmamawa da yabo ga jagoran siyasar mu, Mai Girma Sanata Aliyu Magatakarda Wamako, Sarkin Yamman Sakkwato, wanda hikimarsa, shawarwari da jajircewarsa ga jam’iyyar APC suka taka muhimmiyar rawa wajen gina siyasar Jihar Sakkwato da Arewa gaba daya. Goyon bayansa da jagorancinsa na ci gaba da zama ginshiki ga wannan gwamnati da kuma haske ga sabbin shugabanni masu tasowa.”

 

Mu shiga wannan sabuwar shekara da sabuwar a zama da niyyar ci gaba da goyon bayan shugabanninmu, Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu da Gwamna Ahmed Aliyu yayin da suke kokarin cika alkawurran da suka dauka.

 

Mu zama jakadun zaman lafiya, wakilan ci gaba da kuma gwarazan hadin kai a cikin al’ummominmu.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Next Post
Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Habaka Da Kashi 22% A 2025 Bisa Gagarumar Gudunmawar Bangaren Cartoon

Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Habaka Da Kashi 22% A 2025 Bisa Gagarumar Gudunmawar Bangaren Cartoon

LABARAI MASU NASABA

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.