ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabuwar Shekara: Sanata Danbaba Ya Taya ‘Yan Nijeriya Murna, Ya Yaba Da Jagorancin Tinubu

by Leadership Hausa
5 months ago

Daga Rabi’u Ali Indabawa

Sanata mai wakiltar Mazaɓar Sakkwato ta Kudu a Majalisar Dattawa ta 8 da ta 9, Ibrahim Abdullahi Danbaba Dambuwa (DBB), ya bayyana cewa, shugaba Bola Tinubu ya kudiri aniyar magance dukkan kalubalen da kasar nan ke ciki. Sanata Danbaba ya bayyana haka a cikin sakonsa na taya ‘yan Nijeriya murnar shiga sabuwar shekarar 2026, tare da addu’ar fatan alheri.

 

ADVERTISEMENT

“Yayin da muka shiga sabuwar shekarar 2026, ina mika gaisuwa ta musamman da fatan alheri ga daukacin al’ummar Jihar Sakkwato da kuma ‘yan Nijeriya baki daya. Allah ya sanya wannan shekara ta zama ta sabuwar fata, zaman lafiya da ci gaba mai dorewa ga kasarmu mai albarka,” in ji shi.

  • ’Yansanda Sun Kama Mutane 2 Kan Sace Matan Aure A Kaduna
  • Da Ɗumi-Ɗumi: Chelsea Ta Raba Gari Da Koci Enzo Maresca

Ya ce, “Ina amfani da wannan dama domin taya ‘yan Nijeriya murna da kuma mika gaisuwa ta musamman ga Mai Girma Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, jagora mai jarumta da kishin kasa wanda jajircewarsa wajen sauya fasalin Nijeriya ke kara zaburar da miliyoyin ‘yan kasa.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

 

“Gwamnatin Shugaban Kasa Bola Tinubu ta dauki matakai masu karfi na gyara, duk da kalubale da suka biyo baya, kuma suna gina tubalin sabuwar Njjeriya mai karfi da dogaro da kanta.

 

“Kokarinka a matsayin Shugaban Kasa na farfado da tattalin arziki, karfafa hukumomi da inganta tsaro abin yabo ne. Saboda haka, ina kira ga yan Nijeriya da su ci gaba da nuna hakuri da goyon baya domin ganin wadannan manufofi sun haifar da gagarumin sakamako a nan gaba,” in ji shi.

 

Ya c igaba da cewa; “Ga Mai Girma Gwamnan Jihar Sakkwato, Dr. Ahmed Aliyu (PhD, FCNA, ACIT), ina mika godiya ta musamman bisa jajircewarka wajen ci gaban jiharmu.

 

Ayyukanka a fannonin gine gine, kiwon lafiya, ilimi da tsaro sun nuna hangen nesan ka na gina Sakkwato daya, mai ci gaba da hadin kai. Jagorancinka ya dawo da kuzari a harkokin mulki tare da farfado da fatan al’umma.

 

Haka zalika, ina mika girmamawa da yabo ga jagoran siyasar mu, Mai Girma Sanata Aliyu Magatakarda Wamako, Sarkin Yamman Sakkwato, wanda hikimarsa, shawarwari da jajircewarsa ga jam’iyyar APC suka taka muhimmiyar rawa wajen gina siyasar Jihar Sakkwato da Arewa gaba daya. Goyon bayansa da jagorancinsa na ci gaba da zama ginshiki ga wannan gwamnati da kuma haske ga sabbin shugabanni masu tasowa.”

 

Mu shiga wannan sabuwar shekara da sabuwar a zama da niyyar ci gaba da goyon bayan shugabanninmu, Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu da Gwamna Ahmed Aliyu yayin da suke kokarin cika alkawurran da suka dauka.

 

Mu zama jakadun zaman lafiya, wakilan ci gaba da kuma gwarazan hadin kai a cikin al’ummominmu.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Habaka Da Kashi 22% A 2025 Bisa Gagarumar Gudunmawar Bangaren Cartoon

Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Habaka Da Kashi 22% A 2025 Bisa Gagarumar Gudunmawar Bangaren Cartoon

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.