ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sadio Mane: Daga Ƙwallon Cikin Unguwa Zuwa Zakaran Afirka

by Abba Ibrahim Wada
4 months ago
Sadio

Wannan shi ne karo na biyu da ɗan wasa Sadio Mane ya sake jan ragamar tawagar Senegal zuwa lashe gasar AFCON, amma a wannan karon, ba lashe gasar ba ce kawai ke jan hankali.

Mane, wanda tsohon ɗan wasan Liverpool da Bayern Munich ne, ya lashe gasar AFCON karo na biyu tare da tawagar Senegal, bayan doke Morocco mai masaukin baƙi a wasan da ya haifar da cece-kuce.

Duk wanda ya kalli wasan ƙarshen, ana kusa da tashi wasa ne kocin Senegal Pape Thiaw ya buƙaci ƴan wasansa su fice daga filin wasan bayan da alƙalin wasan ya ba Morocco bugun fanareti a minti na 98 da wasan bayan ɗan wasan baya Senegal El Hadji Malick Douf ya ja Brahim Diaz ya faɗi ƙasa.

ADVERTISEMENT
  • AFCON 2025: CAF Ta Ci Tarar Algeria, Ta Dakatar Da Ƴan Wasanta
  • Yadda Aka Bai Wa Ousmane Dembélé Kyautar Ballon d’Or Ta 2025

Amma a lokacin da ƴan wasan Senegal ke ƙoƙarin ficewa ne aka ga ɗan wasa Sadio Mane yana ta ƙoƙarin lallava su da su koma cikin fili su ci gaba da buga wasan tare da taimakon mai tsaron ragar ƙungiyar, Edourd Mendy.

Kimanin minti 16 bayan lamarin ne Diaz ya buga fanaretin da salon panenka, amma ya zubar, inda Mendy ya kama ƙwallon cikin sauƙi. Bayan an tashi babu ci ne aka shiga ƙarin lokaci, inda Pape Gueye ya zura ƙwallon da ta zama sanadiyar samun nasarar Senegal a kan Morocco mai masaukin baƙi.

LABARAI MASU NASABA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

Xan wasa Mane, wanda ya ce wannan gasar AFCON ta ƙarshe da zai buga, ya nuna bajinta da shugabanci a lokacin da ake buƙata, musamman inda ƴan wasan tawagar suka buƙaci ya wakilce su wajen ɗaga kofi duk da ba shi ba ne kyaftin.

Bayan tashi daga wasan Mane ya ce, “Harkar ƙwallon ƙafa tana da muhimmanci, kuma duniya na kallonmu. Don haka bai kamata mu zama sanadiyyar vata harkar a idon duniya ba.

 

Yaushe Mane Ya Fara Ƙwallo a Senegal?

Sadio Mane ya fara buga ƙwallo ne daga garin Bambali, gari da ke kudu maso yammacin Senegal, inda ya fara ƙwallo a layi a filin turvaya, sannan yana ɗan shekara 13. Mane, wanda yanzu yake buga wasa da ƙungiyar Al-Nassr a Saudiyya, ya samu nasarori da dama, amma duk da haka bai tava mantawa da asalinsa ba.

Yana da ɗimbin masoya a Bambali saboda kyautarsa da ƙoƙarin da yake yi wajen ginawa da gyara asibitoci da makarantu da gina masallatai da ma tallafin da ya bayar a lokacin annobar Korona.

Ƴan uwa da dangi kuma sun bayyana shi a matsayin “wanda yake aiki domin kowa, kuma Musulmin kirki. Haka kuma ya nuna hali na daban a lokacin da yake ƙwallo a Ingila, inda da ya riƙa wanke ban-ɗakunan masallacin Toɗteeth.

Mane ya buga wa Senegal wasa sau 120, inda ya zura ƙwallo 53. Yana nuna ƙwarewa matuƙa a filin wasa, sannan yana da burin wakiltar ƙasarsa a gasar cin kofin duniya da za a buga a bana, inda yake fatan ƙara kafa tarihi.

Ya varar da bugun fanareti a farkon wasan ƙarshe a gasar AFCON ta 2021, amma kuma ya samu nasarar zura bugun fanareti na ƙarshe, inda Ƙasarsa ta lashe gasar ta hanyar doke Masar a birnin Yaounde.

Bayan haka ya kuma jagorancin ƙasarsa wajen doke Masar a wasan cike-gurbi zuwa gasar cin kofin duniya da aka buga a Ƙatar, duk da raunin da ya ji ya hana shi buga gasar.

Duk da cewa Mane ba mutum ba ne mai son girma, kuma ba shi ba ne kyaftin, amma idan ya yi magana, abokan wasansa suna sauraro. A jawabinsa na kafin wasansu da Masar, ya ƙarfafa musu gwiwa. Mane, wanda ya yi zamani ne sosai tare da tsohon kocin tawagar, Aliou Cisse, wanda ya jagoranci tawagar ƙasar tsakanin 2015 zuwa 2024, amma kocin ƙasar na yanzu, Pape Thiaw na da burin ganin ɗan wasan ya ci gaba da wakiltar ƙasar.

Sadio
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?

MASU ALAKA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Next Post
Borge Brende: Kasar Sin Na Son Samar Da Nagartaccen Tasiri Ta Hanyar Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa

Borge Brende: Kasar Sin Na Son Samar Da Nagartaccen Tasiri Ta Hanyar Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.