ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sadio Mane: Daga Ƙwallon Cikin Unguwa Zuwa Zakaran Afirka

by Abba Ibrahim Wada
5 months ago
Sadio

Wannan shi ne karo na biyu da ɗan wasa Sadio Mane ya sake jan ragamar tawagar Senegal zuwa lashe gasar AFCON, amma a wannan karon, ba lashe gasar ba ce kawai ke jan hankali.

Mane, wanda tsohon ɗan wasan Liverpool da Bayern Munich ne, ya lashe gasar AFCON karo na biyu tare da tawagar Senegal, bayan doke Morocco mai masaukin baƙi a wasan da ya haifar da cece-kuce.

Duk wanda ya kalli wasan ƙarshen, ana kusa da tashi wasa ne kocin Senegal Pape Thiaw ya buƙaci ƴan wasansa su fice daga filin wasan bayan da alƙalin wasan ya ba Morocco bugun fanareti a minti na 98 da wasan bayan ɗan wasan baya Senegal El Hadji Malick Douf ya ja Brahim Diaz ya faɗi ƙasa.

ADVERTISEMENT
  • AFCON 2025: CAF Ta Ci Tarar Algeria, Ta Dakatar Da Ƴan Wasanta
  • Yadda Aka Bai Wa Ousmane Dembélé Kyautar Ballon d’Or Ta 2025

Amma a lokacin da ƴan wasan Senegal ke ƙoƙarin ficewa ne aka ga ɗan wasa Sadio Mane yana ta ƙoƙarin lallava su da su koma cikin fili su ci gaba da buga wasan tare da taimakon mai tsaron ragar ƙungiyar, Edourd Mendy.

Kimanin minti 16 bayan lamarin ne Diaz ya buga fanaretin da salon panenka, amma ya zubar, inda Mendy ya kama ƙwallon cikin sauƙi. Bayan an tashi babu ci ne aka shiga ƙarin lokaci, inda Pape Gueye ya zura ƙwallon da ta zama sanadiyar samun nasarar Senegal a kan Morocco mai masaukin baƙi.

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

Xan wasa Mane, wanda ya ce wannan gasar AFCON ta ƙarshe da zai buga, ya nuna bajinta da shugabanci a lokacin da ake buƙata, musamman inda ƴan wasan tawagar suka buƙaci ya wakilce su wajen ɗaga kofi duk da ba shi ba ne kyaftin.

Bayan tashi daga wasan Mane ya ce, “Harkar ƙwallon ƙafa tana da muhimmanci, kuma duniya na kallonmu. Don haka bai kamata mu zama sanadiyyar vata harkar a idon duniya ba.

 

Yaushe Mane Ya Fara Ƙwallo a Senegal?

Sadio Mane ya fara buga ƙwallo ne daga garin Bambali, gari da ke kudu maso yammacin Senegal, inda ya fara ƙwallo a layi a filin turvaya, sannan yana ɗan shekara 13. Mane, wanda yanzu yake buga wasa da ƙungiyar Al-Nassr a Saudiyya, ya samu nasarori da dama, amma duk da haka bai tava mantawa da asalinsa ba.

Yana da ɗimbin masoya a Bambali saboda kyautarsa da ƙoƙarin da yake yi wajen ginawa da gyara asibitoci da makarantu da gina masallatai da ma tallafin da ya bayar a lokacin annobar Korona.

Ƴan uwa da dangi kuma sun bayyana shi a matsayin “wanda yake aiki domin kowa, kuma Musulmin kirki. Haka kuma ya nuna hali na daban a lokacin da yake ƙwallo a Ingila, inda da ya riƙa wanke ban-ɗakunan masallacin Toɗteeth.

Mane ya buga wa Senegal wasa sau 120, inda ya zura ƙwallo 53. Yana nuna ƙwarewa matuƙa a filin wasa, sannan yana da burin wakiltar ƙasarsa a gasar cin kofin duniya da za a buga a bana, inda yake fatan ƙara kafa tarihi.

Ya varar da bugun fanareti a farkon wasan ƙarshe a gasar AFCON ta 2021, amma kuma ya samu nasarar zura bugun fanareti na ƙarshe, inda Ƙasarsa ta lashe gasar ta hanyar doke Masar a birnin Yaounde.

Bayan haka ya kuma jagorancin ƙasarsa wajen doke Masar a wasan cike-gurbi zuwa gasar cin kofin duniya da aka buga a Ƙatar, duk da raunin da ya ji ya hana shi buga gasar.

Duk da cewa Mane ba mutum ba ne mai son girma, kuma ba shi ba ne kyaftin, amma idan ya yi magana, abokan wasansa suna sauraro. A jawabinsa na kafin wasansu da Masar, ya ƙarfafa musu gwiwa. Mane, wanda ya yi zamani ne sosai tare da tsohon kocin tawagar, Aliou Cisse, wanda ya jagoranci tawagar ƙasar tsakanin 2015 zuwa 2024, amma kocin ƙasar na yanzu, Pape Thiaw na da burin ganin ɗan wasan ya ci gaba da wakiltar ƙasar.

Sadio
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
  • Abba Ibrahim Wada
    FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
  • Abba Ibrahim Wada
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

MASU ALAKA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino
Wasanni

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
Wasanni

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

June 22, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
Wasanni

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
Next Post
Borge Brende: Kasar Sin Na Son Samar Da Nagartaccen Tasiri Ta Hanyar Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa

Borge Brende: Kasar Sin Na Son Samar Da Nagartaccen Tasiri Ta Hanyar Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.