ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sadio Mane: Daga Ƙwallon Cikin Unguwa Zuwa Zakaran Afirka

by Abba Ibrahim Wada
6 months ago
Sadio

Wannan shi ne karo na biyu da ɗan wasa Sadio Mane ya sake jan ragamar tawagar Senegal zuwa lashe gasar AFCON, amma a wannan karon, ba lashe gasar ba ce kawai ke jan hankali.

Mane, wanda tsohon ɗan wasan Liverpool da Bayern Munich ne, ya lashe gasar AFCON karo na biyu tare da tawagar Senegal, bayan doke Morocco mai masaukin baƙi a wasan da ya haifar da cece-kuce.

Duk wanda ya kalli wasan ƙarshen, ana kusa da tashi wasa ne kocin Senegal Pape Thiaw ya buƙaci ƴan wasansa su fice daga filin wasan bayan da alƙalin wasan ya ba Morocco bugun fanareti a minti na 98 da wasan bayan ɗan wasan baya Senegal El Hadji Malick Douf ya ja Brahim Diaz ya faɗi ƙasa.

ADVERTISEMENT
  • AFCON 2025: CAF Ta Ci Tarar Algeria, Ta Dakatar Da Ƴan Wasanta
  • Yadda Aka Bai Wa Ousmane Dembélé Kyautar Ballon d’Or Ta 2025

Amma a lokacin da ƴan wasan Senegal ke ƙoƙarin ficewa ne aka ga ɗan wasa Sadio Mane yana ta ƙoƙarin lallava su da su koma cikin fili su ci gaba da buga wasan tare da taimakon mai tsaron ragar ƙungiyar, Edourd Mendy.

Kimanin minti 16 bayan lamarin ne Diaz ya buga fanaretin da salon panenka, amma ya zubar, inda Mendy ya kama ƙwallon cikin sauƙi. Bayan an tashi babu ci ne aka shiga ƙarin lokaci, inda Pape Gueye ya zura ƙwallon da ta zama sanadiyar samun nasarar Senegal a kan Morocco mai masaukin baƙi.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

Xan wasa Mane, wanda ya ce wannan gasar AFCON ta ƙarshe da zai buga, ya nuna bajinta da shugabanci a lokacin da ake buƙata, musamman inda ƴan wasan tawagar suka buƙaci ya wakilce su wajen ɗaga kofi duk da ba shi ba ne kyaftin.

Bayan tashi daga wasan Mane ya ce, “Harkar ƙwallon ƙafa tana da muhimmanci, kuma duniya na kallonmu. Don haka bai kamata mu zama sanadiyyar vata harkar a idon duniya ba.

 

Yaushe Mane Ya Fara Ƙwallo a Senegal?

Sadio Mane ya fara buga ƙwallo ne daga garin Bambali, gari da ke kudu maso yammacin Senegal, inda ya fara ƙwallo a layi a filin turvaya, sannan yana ɗan shekara 13. Mane, wanda yanzu yake buga wasa da ƙungiyar Al-Nassr a Saudiyya, ya samu nasarori da dama, amma duk da haka bai tava mantawa da asalinsa ba.

Yana da ɗimbin masoya a Bambali saboda kyautarsa da ƙoƙarin da yake yi wajen ginawa da gyara asibitoci da makarantu da gina masallatai da ma tallafin da ya bayar a lokacin annobar Korona.

Ƴan uwa da dangi kuma sun bayyana shi a matsayin “wanda yake aiki domin kowa, kuma Musulmin kirki. Haka kuma ya nuna hali na daban a lokacin da yake ƙwallo a Ingila, inda da ya riƙa wanke ban-ɗakunan masallacin Toɗteeth.

Mane ya buga wa Senegal wasa sau 120, inda ya zura ƙwallo 53. Yana nuna ƙwarewa matuƙa a filin wasa, sannan yana da burin wakiltar ƙasarsa a gasar cin kofin duniya da za a buga a bana, inda yake fatan ƙara kafa tarihi.

Ya varar da bugun fanareti a farkon wasan ƙarshe a gasar AFCON ta 2021, amma kuma ya samu nasarar zura bugun fanareti na ƙarshe, inda Ƙasarsa ta lashe gasar ta hanyar doke Masar a birnin Yaounde.

Bayan haka ya kuma jagorancin ƙasarsa wajen doke Masar a wasan cike-gurbi zuwa gasar cin kofin duniya da aka buga a Ƙatar, duk da raunin da ya ji ya hana shi buga gasar.

Duk da cewa Mane ba mutum ba ne mai son girma, kuma ba shi ba ne kyaftin, amma idan ya yi magana, abokan wasansa suna sauraro. A jawabinsa na kafin wasansu da Masar, ya ƙarfafa musu gwiwa. Mane, wanda ya yi zamani ne sosai tare da tsohon kocin tawagar, Aliou Cisse, wanda ya jagoranci tawagar ƙasar tsakanin 2015 zuwa 2024, amma kocin ƙasar na yanzu, Pape Thiaw na da burin ganin ɗan wasan ya ci gaba da wakiltar ƙasar.

Sadio
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?
  • Abba Ibrahim Wada
    Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji
  • Abba Ibrahim Wada
    Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

MASU ALAKA

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
Wasanni

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
Wasanni

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
Wasanni

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Next Post
Borge Brende: Kasar Sin Na Son Samar Da Nagartaccen Tasiri Ta Hanyar Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa

Borge Brende: Kasar Sin Na Son Samar Da Nagartaccen Tasiri Ta Hanyar Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa

LABARAI MASU NASABA

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.