Kungiyar Socio-Economic Rights and Accountability Project (SERAP) ta bukaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya umarci hukumomin da ke kula da shirin tallafin kuɗaɗen talakawa su yi bayani kan yadda aka kashe ko aka yi amfani da sama da Naira biliyan 78.8 na kudaden gwamnati da ake zargin ba a yi cikakken bayani a kansu ba.
SERAP ta ce zarge-zargen sun fito ne daga rahoton Auditor-General na Tarayya na shekarar 2024, wanda aka wallafa ranar 7 ga Agusta 2026. Rahoton ya shafi wasu kudade da aka kashe tsakanin shekarar 2023 zuwa karshen 2024, ciki har da kudaden shirin National Cash Transfer.
Kungiyar ta kuma bukaci gwamnati ta wallafa cikakken bayanin yadda aka raba Naira biliyan 33.751 na tallafin shekarar 2023, ciki har da sunayen wadanda suka amfana, bayanan biyan kudade, tantance wadanda suka cancanta da kuma takardun da suka tabbatar da yadda aka gudanar da rabon.
Bugu da kari, SERAP ta bukaci a binciki wasu kudade da ta ce sun hada da Naira biliyan 36.744 da aka biya ba tare da tantancewa kafin biyan kudin ba, Naira biliyan 4.616 na kashe-kashen da ba su da isassun takardu da suka cike ka’ida, da kuma wasu kudade da suka shafi rajistar masu cin gajiyar shirin, sayen kaya da man dizal.
SERAP ta ce ya kamata hukumomin yaki da cin hanci su gudanar da cikakken bincike kan kudaden da ta bayyana a matsayin wadanda ba a yi cikakken bayani a kansu ba, tare da dawo da duk wani kudin jama’a da aka gano an karkatar ko aka kashe ba bisa ka’ida ba.














