ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Siyasar Gombe: Shin Ko Waƙar Rarara Za Ta Iya Girgizar Tafiyar Pantami

by Bello Hamza
1 month ago
Gombe

A siyasa, ba koyaushe ake cin zaɓe da kuri’u ba; sau da yawa ana fara cin nasara ne ta hanyar rinjayar tunanin al’umma. Duk wanda ya mallaki ajandar tattaunawa, shi ne ke da rinjaye a zuciyar masu sauraro. Wannan shi ne dalilin da ya sa waƙoƙin siyasa suka zama wani muhimmin makami a siyasar Najeriya.

A yau, babu shakka Dauda Kahutu Rarara ya kasance ɗaya daga cikin fitattun mawaƙan siyasa da suka fi iya sauya alkiblar tattaunawar jama’a. Waƙoƙinsa ba wai don nishaɗi kawai ake sauraro ba ne; ana sauraronsu ne domin a gano saƙon siyasa da ke cikinsu. Shi ya sa duk lokacin da ya fitar da waƙa, musamman a lokacin da siyasa ke ɗaukar zafi, mutane kan tsaya su saurara.

Abin da ya faru a Gombe cikin ƴan kwanakin nan ya sake tabbatar da hakan.

ADVERTISEMENT

Ko da yake Rarara bai ambaci sunan kowa kai tsaye ba, masu bibiyar siyasar Gombe sun yi ta fassara waƙoƙinsa da cewa suna nuni ga tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Zamani, Dr. Isa Ali Ibrahim Pantami. Ko wannan fassarar ta yi daidai ko a’a, ba shi ne babban abin dubawa ba. Abin da ya fi muhimmanci shi ne cewa waƙoƙin sun sauya ajandar tattaunawar siyasar jihar.

Tun kafin fitowar waƙoƙin, ana tattauna makomar siyasa Pantami, kalamansa, danfane da yadda yake shagube da kuma kage ga Ƴan adawa. Bayan fitowar waƙoƙin kuwa, tattaunawar ta sauya. An fara magana ne kan hotonsa na siyasa, yadda yake fuskantar suka da kuma tambayoyin da ake tasowa dasu game da shi. Wannan shi ne babban tasirin waƙar siyasa.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

A siyasa, ba koyaushe ake buƙatar tabbatar da zargi kafin ya yi tasiri ba. Abin da ke da muhimmanci shi ne ya zama babban abin tattaunawa. Idan ɗan takara ya shafe lokacinsa yana ƙoƙarin gamsarwa ko kare kansa maimakon gabatar da manufofinsa, to ya riga ya rasa wani ɓangare na filin fafatawa.

Abin da ya sa waƙoƙin Rarara suka fi ɗaukar hankali shi ne yadda suka tilasta wa magoya bayan Pantami fita kafafen sada zumunta domin kare shi. Wannan shi kaɗai alama ce cewa waƙoƙin sun taɓa wata jijiyar siyasa. Da ba su yi tasiri ba, da ba a ga irin wannan gaggawar mayar da martani ba.

Wata muhimmiyar darasi a siyasa ita ce, ba lallai ne wanda ya fara kare kansa ya kasance ya yi laifi ba. Amma idan ya kasa dawo da tattaunawar zuwa kan manufofinsa, abokan hamayyarsa sukan ci gaba da sarrafa ajandar siyasa. Wannan shi ne abin da ke fuskantar Pantami a halin yanzu.

Akwai kuma wani batu da ba za a iya kauce masa ba. Pantami ya fice daga APC yana mai sukar yadda aka gudanar da harkokin cikin gida na jam’iyyar, musamman batun adalci. Yanzu da yake neman jagoranci a wata jam’iyya, sai ya aikata irin abin da ya yi zargi na “rashin adalci”, mutane za su yi masa tambayoyi iri ɗaya da ya riƙa yi wa wasu. Wannan ba zalunci ba ne; wannan shi ne siyasa.

A siyasa, jama’a ba sa son ganin ɗan siyasa yana amfani da ma’auni biyu. Idan ka gina sunanka kan gaskiya da adalci, za a sa ran ka kasance cikin shiri don amsa duk wata tambaya da ta shafi rayuwarka ta siyasa ko ta gwamnati. Wannan shi ne farashin jagoranci.

Haka kuma, fitowar sanarwar wata ƙungiyar fararen hula ta ‘Concerned Gombe Citizens’ a ranar 3 ga Agustan 2026, inda ta buƙaci hukumomin da abin ya shafa su binciki wasu zarge-zargen da ake yaɗawa ya ƙara ɗora batun a gaban jama’a. Ko da yake wannan ba yana nufin an tabbatar da waɗannan zarge-zarge ba ne, kuma bincike ne kaɗai zai iya fayyace gaskiya, amma ta fuskar siyasa, irin waɗannan abubuwa kan ƙara tsawaita muhawara tare da sanya ɗan takara cikin yanayin kare martabarsa kuma hakan na dusashe tasirinsa.

A nan ne tasirin waƙar Rarara ya fito fili. Waƙar ba ita ce ta haifar da waɗannan tambayoyi ba, amma ta taimaka wajen kambama su, da sa su zama babban abin tattaunawa. Wannan shi ne ainihin ƙarfin sadarwar siyasa.

Wani mai sharhi daga Gombe, Tasiu Abubakar, ya bayyana cewa ana bai wa tasirin Pantami girma sosai a shafukan sada zumunta fiye da yadda yake a siyasar cikin gida. A cewarsa, yawancin masu yada saƙonnin siyasar Pantami ba mazauna Gombe ba ne, kuma hakan na iya sa mutane su ɗauka cewa yana da farin jini fiye da yadda yake a zahiri a Jihar Gombe

A siyasar yau, ba wai abin da ka faɗa kaɗai ake saurara ba; abin da mutane suke faɗa a kanka ma yana da tasiri.

Masanin nazarin waƙoƙi da al’adun siyasa, Muhammad Saddiku daga Kaduna, ya bayyana cewa babban ma’aunin tasirin waƙa shi ne irin martanin da take haifarwa. A cewarsa, da ace waƙoƙin ba su da tasiri, da ba za su mamaye tattaunawar kafafen sada zumunta ba. Ya ce yadda magoya baya da masu adawa suka fito suna kare matsayinsu ko kuma suna goyon bayan abin da waƙar ta ƙunsa ya nuna cewa waƙar ta cimma manufarta ta jawo hankalin jama’a.

Wannan shi ya sa ake cewa yaƙin neman zaɓe ba ya fara ranar da INEC ta ce a fara ba. Yana farawa ne daga ranar da al’umma suka fara magana a kanka. A wannan fage kuwa, Rarara ya nuna cewa har yanzu yana da ikon jawo hankalin jama’a da sauya alkiblar tattaunawa.

Ko hakan zai wadatar wajen raunana takarar Pantami? Muhammad Saddiku ya ce, tabbas hakan zai raunana siyasarsa domin a cewarsa siyasa cike take da abubuwan da ke sauyawa cikin gaggawa.

Watsi da tasirin irin waɗannan waƙoƙi, hakan kuskure ne. Tarihin siyasar Najeriya ya nuna cewa waƙoƙin siyasa sun kasance suna taimakawa wajen gina ko raunana hoton ƴan siyasa. Ba sa yanke zaɓe su kaɗai, amma suna iya tasiri kan yadda masu zaɓe ke kallon ɗan takara.

Saboda haka, abin da Rarara ya yi bai kamata a ɗauke shi a matsayin waƙa kawai ba. Dabara ce ta sadarwar siyasa wadda ta samu nasarar sauya abin da ake tattaunawa a Gombe. A maimakon mutane su riƙa magana kan abin da Pantami zai yi idan ya zama gwamna, an fi tattauna yadda yake fuskantar suka da tambayoyin da ake yi masa.

A siyasa, wannan ba ƙaramin sauyi ba ne. Domin duk lokacin da ɗan takara ya daina jagorantar tattaunawa, ya koma bin tattaunawar da wasu suka ƙirƙira masa, to ya shiga yanayin da zai yi ta mayar da martani maimakon gabatar da ajandarsa.

A ƙarshe, ko Pantami zai iya shawo kan wannan ƙalubale ko kuwa waƙoƙin Rarara za su ci gaba da yin tasiri a kansa, lokaci ne zai bayyana. Amma abin da ya riga ya tabbata shi ne cewa Rarara ya sake nuna ƙarfin waƙar siyasa a matsayin makamin yaƙin tunani, domin a siyasa, wanda ya mallaki tunanin jama’a sau da yawa shi ne ke mallakar hanyar zuwa akwatin zaɓe.

Gombe
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Jihar Kano Za Ta Amfana Matuka Da Gidauniyar Aliko Dangote – Masu Ruwa Da Tsaki
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Nuna Damuwa Kan Sake Kamun Da DSS Ta Yi Wa Boɗejo Bayan Samun Belin EFCC
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ba Mu Taba Biyan Kudin Fansa Ba Kuma Ba Za Mu Biya Ba – Kwamishinan Katsina

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Ya Kamata Kasashen Yamma Su Nuna Sahihanci

Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Tarayya Ta Sanya Al'ummomi 944 A Jihohi 21 Cikin Shirin Ko-ta-kwana

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.