Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya miƙa sunan Joseph Olasunkanmi Tegbe domin zama Ministan Wutar Lantarki, bisa amincewar Majalisar Dattawa.
Sanarwar da mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar ta ce an aika da sunan zuwa Majalisar Dattawa domin tantancewa da tabbatarwa kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.
Nadin ya biyo bayan murabus din tsohon ministan, Adebayo Adelabu, wanda ya sauka daga muƙaminsa domin neman kujerar gwamna a Jihar Oyo.
A cewar sanarwar, Tegbe ƙwararre ne a fannin tattalin arziƙi da gyaran tsare-tsare, mai shekaru sama da 35 yana aiki a ɓangarorin gwamnati da masu zaman kansu. Ya taɓa zama babban abokin hulɗa a kamfanin KPMG na Afirka, inda ya jagoranci shirye-shiryen gyaran manufofin kuɗi da sauye-sauyen hukumomi.
Haka kuma, a halin yanzu shi ne Darakta Janar na haɗin gwuiwar Nijeriya da China, kuma ana sa ran naɗin nasa zai ƙara ƙarfafa gyaran ɓangaren wutar lantarki tare da inganta samar da haske da jawo jari a fannin.















Discussion about this post