• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsarin ‘Yancin Kasuwanci A Afirka: Nijeriya Za Ta Amfana Da Dala Biliyan 50 

by Sani Anwar
12 months ago
in Labaran Kasuwanci
0
Tsarin ‘Yancin Kasuwanci A Afirka: Nijeriya Za Ta Amfana Da Dala Biliyan 50 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta jaddada kudirinta na ganin cewa, wasu manya da kananan kamfanoni sun amfana da dala biliyan 50 da aka ware, domin gudanar da tsarin ‘yancin kasuwanci a yankunan Afirka ba tare da fuskantar matsala ba.

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ne ya bayyana haka, a ranar yayin kaddamar da shirin kula da harkokin kasuwanci da aka samar karkashin yankunan kasashen Nahiyar Afirka.

Haka zalika, Shugaban ya bayar da tabbacin cewa; gwamnati za ta ci gaba da tallafa wa kamfanonin Nijeriya a kowane mataki, domin tabbatar da ganin sun ci gajiyar wannan shiri na kasuwancin yankunan kasashen Afirka. “Za a mayar da hankali wajen bin muhimman abubuwan da ke da muhimmanci tare da tabbatar cewa, dukkannin wani kamfani na Nijeriya, tun daga kan kanana da matsakaitan masana’antu har zuwa manyan kamfanoni, za su ci gajiyar wannan yarjejeniya. Saboda haka, gwamnati za ta ci gaba da bayar da tallafin da ya dace, domin saukaka aiwatar da shirin yadda ya kamata, a matkin gida, yanki da kuma nahiyoyi,” in ji shi.

  • Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Sin Da Turai Da Su Aiwatar Da Takara Mai Tsafta Don Cimma Nasara Tare
  • Zamfara Za Ta Bunƙasa Ta Dawo Matsayinta Na Dandalin Kasuwanci A Arewa – Gwamna Dauda

Sannan, ya yi kira da a hada karfi da karfe, domin samun nasarar wannan shiri, yana mai kuma sake jaddada aniyar gwamnatinsa na yin aiki tukuru, domin cimma wannan buri.

“Bari mu sake tabbatar da aniyarmu ta yin nasara a kan wannan shiri na kasuwancin yankunan nahiyar Afirka, ta hanyar yin aiki tare da kuma himma, don cimma ma’ana daya a yayin da muka fara wannan tafiya. Don haka, gwamnatina za ta yi aiki tukuru don ganin kowane dan Nijeriya ya ci gajiyar wannan yarjejeniya mai matukar dimbin tarihi. Har ila yau, bari in kara da cewa; za a karfafa tsarin hukumomi da na doka, don taimakawa wajen cimma wadannan manufofi,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya

Haka zalika, sakamakon kaddamar da wannan shiri na kasuwanci, Tinubu ya bayyana wani gagarumin ci gaba da aka samu, inda ya zayyana shi a matsayin wani abu wanda zai haifar da harkokin kasuwanci tsakanin kasashen Afirka tare kuma habaka tattalin arziki da kuma ci gaba mai dorewa.

Tinubu ya kara da cewa, dandalin zai bude sabbin kasuwanni ga kayayyaki ko hajojin Nijeriya tare da kara samar da gasa da kuma ayyukan yi.

Ko’odinata na kungiyar ta kasa, Mista Olusegun Awolowo; ya jaddada cewa, jarjejeniyar na da matukar amfani musamman ga dimbin albarkatun Afirka wajen sanya masana’antu da al’ummar matasa cikin tsarin tare kuma da saukaka ci gaban tattalin arziki.

Har ila yau, Awolowo ya jaddada cewa, kasuwanci ne hanya mafi dorewa wajen samun wadata, sannan ya bukaci Nijeriya da sauran kasashen Afirka da su yi kokarin samar da hanyoyin fita daga cikin kangin talauci, rashin aikin yi da kuma tabarbarewar matsalar tattalin arziki.

“A yau, bayan cika dukkanin sharadodin yarjejeniya da aka tsara don, tabbatar da wannan shiri na kasuwanci; mun tsaya a matsayinmu na shaida kan yadda za a aiwatar da wannan kasuwanci a hukumance, a karkashin wannan tsari na ciniki na musamman tare da jigilar kaya daga tashar jiragen ruwa na Apapa,” in ji Awolowo.

Haka nan, Awolowon ya bayyana cewa; bayan kaddamar da aikin a hukumance, kamfanoni goma ne za su fara fitar da kayayyakin Nijeriya zuwa kasashen biyar gabashi, tsakiya da kuma Arewacin Afirka.

“Wasu daga cikin kamfanonin sun hada da kamfanin ‘Le Look Nigeria Limited’, wanda zai fitar da jakunkunan zuwa Kasar Kenya tare da wakiltar dukkanin ‘yan kasuwa mata, sai kamfanin ‘Secure ID Limited’, wanda zai fitar katin na musamman zuwa Kasar Kamaru, sai kuma kamfanin Dangote shi ma da zai fitar da kayan zuwa Kasar ta Kamaru,” kamar yadda ya bayyana.

Ministar Masana’antu, Ciniki da Zuba Jari, Doris Uzoka-Anite, ta nanata kudirin Nijeriya na ci gaba da kuma gagarumin alkawarin da yankunan kasashen Afirkan suka yi na bunkasa ci gaban masana’antu.

Sannan, ta yi kira ga masu ruwa da tsaki das u hada karfi da karfe wajen tabbatar da samar da ayyukan yi ga jama’a, tare kuma da yin amfani da dandalin wajen amfani da damammakin da ake da su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AfrikaKasuwanciNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hanyoyin Dakile Ta’addanci Da ‘Yan Ta’adda

Next Post

Darasi Daga Suratun Najmi (3): Ayoyin Allah Da Annabi (SAW) Ya Gani

Related

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025
Labaran Kasuwanci

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

12 hours ago
Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya
Labaran Kasuwanci

Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya

3 weeks ago
Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman
Labaran Kasuwanci

Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman

6 months ago
Alternative Bank Shi Ne Mafi Inganci Da Baya Amfani Da Kuɗin Ruwa Da Zuwa Da Fasaha A 2024
Labarai

Alternative Bank Shi Ne Mafi Inganci Da Baya Amfani Da Kuɗin Ruwa Da Zuwa Da Fasaha A 2024

7 months ago
Kamfanin NNPCL Zai Cefanar Da Matatun Mai Na Kaduna Da Warri
Labarai

Kamfanin NNPCL Zai Cefanar Da Matatun Mai Na Kaduna Da Warri

10 months ago
Ministan Ma’adanai Ya Bukaci Masu Harkar Ma’adanai A Jihar Nasarawa Su Zauna Lafiya
Labaran Kasuwanci

Ministan Ma’adanai Ya Bukaci Masu Harkar Ma’adanai A Jihar Nasarawa Su Zauna Lafiya

10 months ago
Next Post
Darasi Daga Suratun Najmi (3): Ayoyin Allah Da Annabi (SAW) Ya Gani

Darasi Daga Suratun Najmi (3): Ayoyin Allah Da Annabi (SAW) Ya Gani

LABARAI MASU NASABA

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

July 12, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

July 12, 2025
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

July 12, 2025
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

July 12, 2025
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

July 12, 2025
Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.