ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsarin ‘Yancin Kasuwanci A Afirka: Nijeriya Za Ta Amfana Da Dala Biliyan 50 

by Sani Anwar
2 years ago
Kasuwanci

Gwamnatin tarayya ta jaddada kudirinta na ganin cewa, wasu manya da kananan kamfanoni sun amfana da dala biliyan 50 da aka ware, domin gudanar da tsarin ‘yancin kasuwanci a yankunan Afirka ba tare da fuskantar matsala ba.

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ne ya bayyana haka, a ranar yayin kaddamar da shirin kula da harkokin kasuwanci da aka samar karkashin yankunan kasashen Nahiyar Afirka.

Haka zalika, Shugaban ya bayar da tabbacin cewa; gwamnati za ta ci gaba da tallafa wa kamfanonin Nijeriya a kowane mataki, domin tabbatar da ganin sun ci gajiyar wannan shiri na kasuwancin yankunan kasashen Afirka. “Za a mayar da hankali wajen bin muhimman abubuwan da ke da muhimmanci tare da tabbatar cewa, dukkannin wani kamfani na Nijeriya, tun daga kan kanana da matsakaitan masana’antu har zuwa manyan kamfanoni, za su ci gajiyar wannan yarjejeniya. Saboda haka, gwamnati za ta ci gaba da bayar da tallafin da ya dace, domin saukaka aiwatar da shirin yadda ya kamata, a matkin gida, yanki da kuma nahiyoyi,” in ji shi.

ADVERTISEMENT
  • Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Sin Da Turai Da Su Aiwatar Da Takara Mai Tsafta Don Cimma Nasara Tare
  • Zamfara Za Ta Bunƙasa Ta Dawo Matsayinta Na Dandalin Kasuwanci A Arewa – Gwamna Dauda

Sannan, ya yi kira da a hada karfi da karfe, domin samun nasarar wannan shiri, yana mai kuma sake jaddada aniyar gwamnatinsa na yin aiki tukuru, domin cimma wannan buri.

“Bari mu sake tabbatar da aniyarmu ta yin nasara a kan wannan shiri na kasuwancin yankunan nahiyar Afirka, ta hanyar yin aiki tare da kuma himma, don cimma ma’ana daya a yayin da muka fara wannan tafiya. Don haka, gwamnatina za ta yi aiki tukuru don ganin kowane dan Nijeriya ya ci gajiyar wannan yarjejeniya mai matukar dimbin tarihi. Har ila yau, bari in kara da cewa; za a karfafa tsarin hukumomi da na doka, don taimakawa wajen cimma wadannan manufofi,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta

Haka zalika, sakamakon kaddamar da wannan shiri na kasuwanci, Tinubu ya bayyana wani gagarumin ci gaba da aka samu, inda ya zayyana shi a matsayin wani abu wanda zai haifar da harkokin kasuwanci tsakanin kasashen Afirka tare kuma habaka tattalin arziki da kuma ci gaba mai dorewa.

Tinubu ya kara da cewa, dandalin zai bude sabbin kasuwanni ga kayayyaki ko hajojin Nijeriya tare da kara samar da gasa da kuma ayyukan yi.

Ko’odinata na kungiyar ta kasa, Mista Olusegun Awolowo; ya jaddada cewa, jarjejeniyar na da matukar amfani musamman ga dimbin albarkatun Afirka wajen sanya masana’antu da al’ummar matasa cikin tsarin tare kuma da saukaka ci gaban tattalin arziki.

Har ila yau, Awolowo ya jaddada cewa, kasuwanci ne hanya mafi dorewa wajen samun wadata, sannan ya bukaci Nijeriya da sauran kasashen Afirka da su yi kokarin samar da hanyoyin fita daga cikin kangin talauci, rashin aikin yi da kuma tabarbarewar matsalar tattalin arziki.

“A yau, bayan cika dukkanin sharadodin yarjejeniya da aka tsara don, tabbatar da wannan shiri na kasuwanci; mun tsaya a matsayinmu na shaida kan yadda za a aiwatar da wannan kasuwanci a hukumance, a karkashin wannan tsari na ciniki na musamman tare da jigilar kaya daga tashar jiragen ruwa na Apapa,” in ji Awolowo.

Haka nan, Awolowon ya bayyana cewa; bayan kaddamar da aikin a hukumance, kamfanoni goma ne za su fara fitar da kayayyakin Nijeriya zuwa kasashen biyar gabashi, tsakiya da kuma Arewacin Afirka.

“Wasu daga cikin kamfanonin sun hada da kamfanin ‘Le Look Nigeria Limited’, wanda zai fitar da jakunkunan zuwa Kasar Kenya tare da wakiltar dukkanin ‘yan kasuwa mata, sai kamfanin ‘Secure ID Limited’, wanda zai fitar katin na musamman zuwa Kasar Kamaru, sai kuma kamfanin Dangote shi ma da zai fitar da kayan zuwa Kasar ta Kamaru,” kamar yadda ya bayyana.

Ministar Masana’antu, Ciniki da Zuba Jari, Doris Uzoka-Anite, ta nanata kudirin Nijeriya na ci gaba da kuma gagarumin alkawarin da yankunan kasashen Afirkan suka yi na bunkasa ci gaban masana’antu.

Sannan, ta yi kira ga masu ruwa da tsaki das u hada karfi da karfe wajen tabbatar da samar da ayyukan yi ga jama’a, tare kuma da yin amfani da dandalin wajen amfani da damammakin da ake da su.

Kasuwanci
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta
Labaran Kasuwanci

Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta

May 29, 2026
Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA
Labaran Kasuwanci

Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA

May 21, 2026
Next Post
Darasi Daga Suratun Najmi (3): Ayoyin Allah Da Annabi (SAW) Ya Gani

Darasi Daga Suratun Najmi (3): Ayoyin Allah Da Annabi (SAW) Ya Gani

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.