ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Miliyoyin Yaran Nijeriya Ke Fama Da Aikatau

Mun wallafa a ranar 29 ga Satumba, 2023

by Leadership Hausa
3 years ago
Aikatau

Labarun yadda ake cin zarafin yara masu aikatau a sassan Nijeriya na da tayar da hankula. Yara kan yi aiki ne ba dare ba rana yayin da masu gidansu ke musguna musu. Ana biyan su abin da bai taka kara ya karya ba a wasu wuraren ma ba a biyansu ko kwabo. Ba wai yaki ne ya ci rayukan iyayensu ba, amma iyayen nasu ne suka mika su ga masu safarar su zuwa wajen aikatau din saboda tsanannin matsalar tattalin arzkin da suke ciki.

Dan abincin da aka rage suke samu su ci, shi ne kuma kadai abin da ke kwantar musu da hankali.

  • NAF Ta Lalata Haramtattun Wuraren Tace Mai Guda 6 A Ribas 
  • Boss Mustapha Ya Karyata Zargin Satar Dala Miliyan 6.3 Daga CBN

Binciken da jaridar LEADERSHIP Hausa ta yi, ya nuna cewa, daukar yara aikin aikatau yana matukar karuwa a ‘yan shekarun nan a sassan Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Labaran halin da yara masu aikatau ke ciki yana tayar da hakula, yana kara nuna irin muguntan da ake nuna wa yara ‘yan aiki a gidajen da suke zaman aikatau.

Labarin Bolutife, ‘yar shekara 13, ta uku ga wasu iyalai matalauta a garin Akure ta Jihar Ondo, lamarinta tamkar iyayenta sun mika ta zuwa rayuwar bauta ne da kansu. A ranar da abin ya faru, wata rana ce a watan Yuni na shekarar 2022, ta ga mahaifinta mai suna Olumide, dan shekara 54, yana tattauanwa da wasu baki daga Abuja a cikin falon gidansu. Daga baya ta fahinci cewa sune wadanda za su dauke ta aiki sune kuma za su ci gaba da cin zarafinta. Bolutife ta zama ‘yar aiki kuma baiwa haka kuma wanda ya dauke aiki ya zama da ita tamkar matarsa yana lalata da ita a kan dan abin da bai taka kara ya karya ba da yake ba iyayenta.

LABARAI MASU NASABA

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

A halin yanzu tana nan ta fara farfadowa bayan da ta yi wata 8 ana musguna mata. Ta samu ‘yanci ne bayan da wata kungiya mai zaman kanta ta ceto ta.

Amma ba duka suke samun irin wannan sa’ar ba, misali, labarin Jemilah ya fara ne a ranar 7 ga watan Yuli na shekarar 2016 a garin Legas inda mutumin da ta ke yi wa aiki cikin fushi saboda bata wake buta yadda yake so ba ya ji mata ciwon da ya kai ga makancewarta a ido daya har a abada. Abin takaicin shi ne yarinyar ‘yar shekara 12 ta yi kokarinta na ganin ta ganmsar da uban dakin nata amma shi bai gani ba.

A wani lamari kuma da ya faru a garin Ikorodu ta Jihar Legas a ranar 19 ga watan Disamba 2016, wata mata mai yara uku wadda ya kamata ta zama mai kare rayuwa tare da shiryar da yara kamar yadda take yi wa yaranta amma sai ta zama sanadiyyar mutuwar ‘yar aikinta mai suna Faith, ‘yar shekara 10. Wannan lamarin ya tayar da hakulan al’umma kwarai da gaske.

Haka kuma a ranar 20 ga watan Mayu 2017. Wata ‘yar kasuwa ta yi wa ‘yar aikinta dukan kawo wuka inda dukan ya yi sanadiyyar mutuwarta, matar wadda ke daukje da ciki ta yi kokarin batar da gawar yarinyar amma asirinta ya tonu, daga nan doka ta yi halinta a kanta

Bincike ya kuma nuna yadda a watan Maris na shekarar 2018, aka samu irin wannan lamarin a birnin Legas, inda wata ‘yar aiki mai shgkara 10 a duniya ta kusan shekawa barzahu, laifinta kwai shi ne ta yi kokarin fada da yaran wadanda suka dauke ta aiki. Amma hukuncin da aka yi mata ya fi ainihin laifin da ta yi don kuwa an yi amfani da dutsen guga ne mai zafi ana dosanata mata a jiki, inda ya haifar da tabo masu yawa a jikinta.

An kuma samu irin wannan labarin a ranar 23 ga watan Afrilu na shekakar 2018, a Jihar Anambara, inda wata mai suna Uche Ugochukwu ta fito da maitarta da kuma tsananin muguntanta a kan ‘yar aikinta mai shekara 12, ta yi mata dukan kawo wuka abin da ya yi sanadiyyar ji mata ciwo a cikinta ya haifar mata da ciwon da za ta gama rayuwarta da su don ya shafi mahaifarta da wasu sassan hanjinta gaba daya.

Kididdiga daga Hukumar Kwadago ta Duniya (ILO), ya nuna cewa, yara fiye da Miliyan 15 ke aikin aikatau a Nijeriya. Aikatau na yara na nufin duk wani aiki da za a iya sa yara da zai hana su cin gajiyar yarintarsu, wanda kuma zai iya hana su halartar makaranta a lokacin da ya dace wanda kuma zai iya cutar da su ta kowacce hanya, kamar yadda kundin Wikipedia na shekarar 2022 ya zayyana.

Aikatau
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
  • Leadership Hausa
    Batun Dawo Da Tallafin Mai Da Atiku Ya Yi Na Ci Gaba Da Tayar Da Kura
  • Leadership Hausa
    Batun Guguwar Kakar Yakin Neman Zabukan 2027 A Nijeriya

MASU ALAKA

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Umarnin Kawo Karshen Matsalar Tsaro
Rahotonni

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

September 5, 2026
Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
Rahotonni

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

September 5, 2026
Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
Rahotonni

Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki

September 5, 2026
Next Post
Yankunan Raya Tattalin Arziki Na Sin Sun Samu Ci Gaban GDP A 2022

Yankunan Raya Tattalin Arziki Na Sin Sun Samu Ci Gaban GDP A 2022

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.