ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Miliyoyin Yaran Nijeriya Ke Fama Da Aikatau

Mun wallafa a ranar 29 ga Satumba, 2023

by Leadership Hausa
3 years ago
Aikatau

Labarun yadda ake cin zarafin yara masu aikatau a sassan Nijeriya na da tayar da hankula. Yara kan yi aiki ne ba dare ba rana yayin da masu gidansu ke musguna musu. Ana biyan su abin da bai taka kara ya karya ba a wasu wuraren ma ba a biyansu ko kwabo. Ba wai yaki ne ya ci rayukan iyayensu ba, amma iyayen nasu ne suka mika su ga masu safarar su zuwa wajen aikatau din saboda tsanannin matsalar tattalin arzkin da suke ciki.

Dan abincin da aka rage suke samu su ci, shi ne kuma kadai abin da ke kwantar musu da hankali.

  • NAF Ta Lalata Haramtattun Wuraren Tace Mai Guda 6 A Ribas 
  • Boss Mustapha Ya Karyata Zargin Satar Dala Miliyan 6.3 Daga CBN

Binciken da jaridar LEADERSHIP Hausa ta yi, ya nuna cewa, daukar yara aikin aikatau yana matukar karuwa a ‘yan shekarun nan a sassan Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Labaran halin da yara masu aikatau ke ciki yana tayar da hakula, yana kara nuna irin muguntan da ake nuna wa yara ‘yan aiki a gidajen da suke zaman aikatau.

Labarin Bolutife, ‘yar shekara 13, ta uku ga wasu iyalai matalauta a garin Akure ta Jihar Ondo, lamarinta tamkar iyayenta sun mika ta zuwa rayuwar bauta ne da kansu. A ranar da abin ya faru, wata rana ce a watan Yuni na shekarar 2022, ta ga mahaifinta mai suna Olumide, dan shekara 54, yana tattauanwa da wasu baki daga Abuja a cikin falon gidansu. Daga baya ta fahinci cewa sune wadanda za su dauke ta aiki sune kuma za su ci gaba da cin zarafinta. Bolutife ta zama ‘yar aiki kuma baiwa haka kuma wanda ya dauke aiki ya zama da ita tamkar matarsa yana lalata da ita a kan dan abin da bai taka kara ya karya ba da yake ba iyayenta.

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

A halin yanzu tana nan ta fara farfadowa bayan da ta yi wata 8 ana musguna mata. Ta samu ‘yanci ne bayan da wata kungiya mai zaman kanta ta ceto ta.

Amma ba duka suke samun irin wannan sa’ar ba, misali, labarin Jemilah ya fara ne a ranar 7 ga watan Yuli na shekarar 2016 a garin Legas inda mutumin da ta ke yi wa aiki cikin fushi saboda bata wake buta yadda yake so ba ya ji mata ciwon da ya kai ga makancewarta a ido daya har a abada. Abin takaicin shi ne yarinyar ‘yar shekara 12 ta yi kokarinta na ganin ta ganmsar da uban dakin nata amma shi bai gani ba.

A wani lamari kuma da ya faru a garin Ikorodu ta Jihar Legas a ranar 19 ga watan Disamba 2016, wata mata mai yara uku wadda ya kamata ta zama mai kare rayuwa tare da shiryar da yara kamar yadda take yi wa yaranta amma sai ta zama sanadiyyar mutuwar ‘yar aikinta mai suna Faith, ‘yar shekara 10. Wannan lamarin ya tayar da hakulan al’umma kwarai da gaske.

Haka kuma a ranar 20 ga watan Mayu 2017. Wata ‘yar kasuwa ta yi wa ‘yar aikinta dukan kawo wuka inda dukan ya yi sanadiyyar mutuwarta, matar wadda ke daukje da ciki ta yi kokarin batar da gawar yarinyar amma asirinta ya tonu, daga nan doka ta yi halinta a kanta

Bincike ya kuma nuna yadda a watan Maris na shekarar 2018, aka samu irin wannan lamarin a birnin Legas, inda wata ‘yar aiki mai shgkara 10 a duniya ta kusan shekawa barzahu, laifinta kwai shi ne ta yi kokarin fada da yaran wadanda suka dauke ta aiki. Amma hukuncin da aka yi mata ya fi ainihin laifin da ta yi don kuwa an yi amfani da dutsen guga ne mai zafi ana dosanata mata a jiki, inda ya haifar da tabo masu yawa a jikinta.

An kuma samu irin wannan labarin a ranar 23 ga watan Afrilu na shekakar 2018, a Jihar Anambara, inda wata mai suna Uche Ugochukwu ta fito da maitarta da kuma tsananin muguntanta a kan ‘yar aikinta mai shekara 12, ta yi mata dukan kawo wuka abin da ya yi sanadiyyar ji mata ciwo a cikinta ya haifar mata da ciwon da za ta gama rayuwarta da su don ya shafi mahaifarta da wasu sassan hanjinta gaba daya.

Kididdiga daga Hukumar Kwadago ta Duniya (ILO), ya nuna cewa, yara fiye da Miliyan 15 ke aikin aikatau a Nijeriya. Aikatau na yara na nufin duk wani aiki da za a iya sa yara da zai hana su cin gajiyar yarintarsu, wanda kuma zai iya hana su halartar makaranta a lokacin da ya dace wanda kuma zai iya cutar da su ta kowacce hanya, kamar yadda kundin Wikipedia na shekarar 2022 ya zayyana.

Aikatau
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
Yankunan Raya Tattalin Arziki Na Sin Sun Samu Ci Gaban GDP A 2022

Yankunan Raya Tattalin Arziki Na Sin Sun Samu Ci Gaban GDP A 2022

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.