ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yakin Ciniki Kalubale Ne Kuma Dama Ce Ga Nahiyar Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Ciniki

Yakin cinikin da kasar Amurka ta tayar kalubale ne ga kasashen Afirka, amma kuma dama ce gare su, ta la’akari da yanayi mai armashi da huldar Afirka da Sin ke ciki, musamman ma ta fuskar cinikayya. Wannan ya riga ya zama ra’ayin bai daya na mutanen Sin da na kasashen Afirka.

 

Kwanan baya, kungiyar ciniki ta duniya WTO ta gabatar da rahoton hasashen yanayin ciniki na duniya, inda ta ce matakin karbar karin harajin kwastam da kasar Amurka ta dauka, da sauran manufofin kasar marasa tabbas, za su iya haddasa raguwar cinikin kayayyaki da ta kai kaso 1.5% a duniya, lamarin da zai illata kasashe marasa karfin tattalin arziki, wadanda ke dogaro kan sayar da kayayyaki ga kasashen ketare.

ADVERTISEMENT
  • Za A Yi Jana’izar Fafaroma Francis A Ranar Asabar A Vatican
  • Gwamnan Edo Ya Dakatar da Sarki Saboda Matsalar Tsaro A Yankinsa

Yayin da Ngozi Okonjo-Iweala, babbar darektar kungiyar ta WTO ke gabatar da wannan rahoto, ta ambaci misalin kasar Lesotho. A matsayin daya daga cikin kasashen dake dogaro kan fitar da kayayyaki zuwa waje, kasar Lesotho ta fitar da kayayyakin da darajarsu ta kai dalar Amurka miliyan 237 a duk shekara ga kasar Amurka, wadanda yawancinsu lu’u-lu’u, da yadi mai kwari ne. A cewar mujallar Foreign Policy ta kasar Amurka, ta la’akari da raunin tattalin arzikin kasar Lesotho, inda matsakaicin kudin shigar duk mutum daya bai wuce dala 975 a shekara daya ba, kudin harajin kwastam na kaso 50% da kasar Amurka ta yi shirin kakaba wa kasar, zai iya haifar da barna ga tattalin arzikinta.

 

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

Sai dai a hakika, ba dole ne kasar Lesotho, da sauran kasashen Afirka su mika wuya ga kasar Amurka, don ta ci zalinsu yadda ta ga dama ba. Kamar yadda Charles Olunaiju, wani masanin kasar Najeriya, ya rubuta a cikin wata makalarsa da jaridar Vanguard ta wallafa, kasar Amurka ba za ta samu biyan bukata a yakin ciniki da ta tayar ba, saboda dunkulewar duniya sakamakon dimbin cinikin da ake yi tsakanin kasashe daban daban, da hadewar sassan duniya da cudanyar mabambantan al’adu, wadanda aka samu bisa tushen ci gaban fasahohi, sun haifar da wani yanayi mai armashi da ba za a iya sauya shi ba.

 

Mista Olunaiju ya kara da cewa, a matsayin wata dabarar tinkarar rikici, kasashen Afirka za su iya amfani da tsarin yankin ciniki mai ‘yanci na nahiyar Afirka (AfCFTA) wajen mai da nahiyar dunkulallun kasuwanni, da babban yankin da ake zuba masa jari, ta yadda za a ba kasashen Afirka damar aiwatar da Ajandar Raya Kasa ta 2063 yadda ake bukata. A sa’i daya kuma, kasar Sin, bisa matsayinta na abokiyar hulda mafi muhimmanci a fannin cinikayya ga kasashen Afirka, za ta samar da taimako ga nahiyar Afirka a kokarinsu na tabbatar da zaman lafiya, da walwala, in ji Mista Olunaiju.

 

Sa’an nan, a nasa bangare, Dennis Mwaniki, shahararren mai nazarin manufofin hukumomi dan kasar Kenya, yana da ra’ayin iri daya dangane da yakin cinikin da kasar Amurka ta kaddamar, inda ya ce, matsin lamba da Amurka ta dora wa kasashen Afirka zai sa su kara karkata ga kasar Sin, da sauran manyan tattalin arziki dake tasowa. Saboda yayin da kasar Amurka ke rufe kofarta, sauran kasashe sun ba da karin damammakin kulla huldar ciniki, wadda za ta samar da sakamako mai gamsarwa. Sabanin matakin kasar Amurka na karbar karin harajin kwastam, kasar Sin ta yafe wa kasashe masu raunin tattalin arziki harajin kwastam, da ba su sauran tallafi da gatanci, lamarin da ya janyo hankalin dimbin ‘yan kasuwan kasashen Afirka ga kasuwannin kasar Sin mai yawan al’umma da ya kai biliyan 1.4. Mista Mwaniki ya jaddada cewa, “Wannan tsari zai tabbatar da moriyar kowa, ba kamar manufar da Donald Trump ya daukaka ta Cin Moriya daga Faduwar Wani ba.”

 

Ban da haka, jawabin da jakadan kasar Sin a Najeriya Yu Dunhai ya yi, a birnin Abuja a kwanan baya, ya zama mai goyon bayan maganganun da masanan kasashen Afirka suka fada, inda jakadan ya ce, ya kamata a kalli yakin ciniki a matsayin wata damar karfafa huldar hadin kai tsakanin kasashen Sin da Najeriya, gami da tsakanin Sin da kasashen Afirka baki daya. Yanzu kasashen Afirka na kokarin farfado da tattalin arzikinsu, saboda haka suna bukatar tsarin ciniki mai ‘yanci da ya shafi bangarori daban daban, da wani muhallin kasuwanci da ake iya hasashen yanayinsa na nan gaba. Yayin da kasar Sin a nata bangare take dukufa wajen bude kofarta ga kasashen ketare, da kokarin taimakon kasashen Afirka wajen raya kansu a kai a kai, matakan da ke da muhimmanci ga yunkurin saukaka yanayin rashin tabbas da ake fuskantar sakamakon yakin ciniki.

 

Sai dai wadanne matakai ne za a iya dauka don tinkarar yakin ciniki? Za mu iya ci gaba da daukar misalin kasar Lesotho, inda kayayyakin da take fitarwa kasar Amurka, idan Amurka ba ta so, to, za a iya bin shawarar Madam Ngozi Iweala, wadda ta ce sai a sayar da su ga sauran kasashen dake nahiyar Afirka. Ban da haka, kasar Lesotho za ta iya hadin gwiwa da kasar Sin wajen inganta tsarin masana’antu, ta yadda za ta lalubo sabuwar damar ciniki. Ganin yadda kasar Sin ta zama kasa ta farko da ta kulla huldar hadin kai bisa manyan tsare-tsare tare da Lesotho, kana adadin cinikin da ake yi tsakanin kasashen 2 ya riga ya karu zuwa dala miliyan 150 a bara.

 

Sinawa kan ce, “Dabara ta fi matsala yawa.” Mu yi kokarin tinkarar kalubale, ta yadda za a iya mayar da shi damar raya kai. (Bello Wang)

Ciniki
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Ciniki
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Illolin Da Manufar Haraji Kan Kayayyaki Ta Haifar A Kan Amerikawa

Illolin Da Manufar Haraji Kan Kayayyaki Ta Haifar A Kan Amerikawa

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.