• English
  • Business News
Thursday, May 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yakin Ciniki Kalubale Ne Kuma Dama Ce Ga Nahiyar Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 weeks ago
in Ra'ayi Riga
0
Yakin Ciniki Kalubale Ne Kuma Dama Ce Ga Nahiyar Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yakin cinikin da kasar Amurka ta tayar kalubale ne ga kasashen Afirka, amma kuma dama ce gare su, ta la’akari da yanayi mai armashi da huldar Afirka da Sin ke ciki, musamman ma ta fuskar cinikayya. Wannan ya riga ya zama ra’ayin bai daya na mutanen Sin da na kasashen Afirka.

 

Kwanan baya, kungiyar ciniki ta duniya WTO ta gabatar da rahoton hasashen yanayin ciniki na duniya, inda ta ce matakin karbar karin harajin kwastam da kasar Amurka ta dauka, da sauran manufofin kasar marasa tabbas, za su iya haddasa raguwar cinikin kayayyaki da ta kai kaso 1.5% a duniya, lamarin da zai illata kasashe marasa karfin tattalin arziki, wadanda ke dogaro kan sayar da kayayyaki ga kasashen ketare.

  • Za A Yi Jana’izar Fafaroma Francis A Ranar Asabar A Vatican
  • Gwamnan Edo Ya Dakatar da Sarki Saboda Matsalar Tsaro A Yankinsa

Yayin da Ngozi Okonjo-Iweala, babbar darektar kungiyar ta WTO ke gabatar da wannan rahoto, ta ambaci misalin kasar Lesotho. A matsayin daya daga cikin kasashen dake dogaro kan fitar da kayayyaki zuwa waje, kasar Lesotho ta fitar da kayayyakin da darajarsu ta kai dalar Amurka miliyan 237 a duk shekara ga kasar Amurka, wadanda yawancinsu lu’u-lu’u, da yadi mai kwari ne. A cewar mujallar Foreign Policy ta kasar Amurka, ta la’akari da raunin tattalin arzikin kasar Lesotho, inda matsakaicin kudin shigar duk mutum daya bai wuce dala 975 a shekara daya ba, kudin harajin kwastam na kaso 50% da kasar Amurka ta yi shirin kakaba wa kasar, zai iya haifar da barna ga tattalin arzikinta.

 

Labarai Masu Nasaba

Sara Da Sassaka Ba Ya Hana Gamji Toho

Raya Kasa Na Bukatar Bin Daidaitacciyar Hanya

Sai dai a hakika, ba dole ne kasar Lesotho, da sauran kasashen Afirka su mika wuya ga kasar Amurka, don ta ci zalinsu yadda ta ga dama ba. Kamar yadda Charles Olunaiju, wani masanin kasar Najeriya, ya rubuta a cikin wata makalarsa da jaridar Vanguard ta wallafa, kasar Amurka ba za ta samu biyan bukata a yakin ciniki da ta tayar ba, saboda dunkulewar duniya sakamakon dimbin cinikin da ake yi tsakanin kasashe daban daban, da hadewar sassan duniya da cudanyar mabambantan al’adu, wadanda aka samu bisa tushen ci gaban fasahohi, sun haifar da wani yanayi mai armashi da ba za a iya sauya shi ba.

 

Mista Olunaiju ya kara da cewa, a matsayin wata dabarar tinkarar rikici, kasashen Afirka za su iya amfani da tsarin yankin ciniki mai ‘yanci na nahiyar Afirka (AfCFTA) wajen mai da nahiyar dunkulallun kasuwanni, da babban yankin da ake zuba masa jari, ta yadda za a ba kasashen Afirka damar aiwatar da Ajandar Raya Kasa ta 2063 yadda ake bukata. A sa’i daya kuma, kasar Sin, bisa matsayinta na abokiyar hulda mafi muhimmanci a fannin cinikayya ga kasashen Afirka, za ta samar da taimako ga nahiyar Afirka a kokarinsu na tabbatar da zaman lafiya, da walwala, in ji Mista Olunaiju.

 

Sa’an nan, a nasa bangare, Dennis Mwaniki, shahararren mai nazarin manufofin hukumomi dan kasar Kenya, yana da ra’ayin iri daya dangane da yakin cinikin da kasar Amurka ta kaddamar, inda ya ce, matsin lamba da Amurka ta dora wa kasashen Afirka zai sa su kara karkata ga kasar Sin, da sauran manyan tattalin arziki dake tasowa. Saboda yayin da kasar Amurka ke rufe kofarta, sauran kasashe sun ba da karin damammakin kulla huldar ciniki, wadda za ta samar da sakamako mai gamsarwa. Sabanin matakin kasar Amurka na karbar karin harajin kwastam, kasar Sin ta yafe wa kasashe masu raunin tattalin arziki harajin kwastam, da ba su sauran tallafi da gatanci, lamarin da ya janyo hankalin dimbin ‘yan kasuwan kasashen Afirka ga kasuwannin kasar Sin mai yawan al’umma da ya kai biliyan 1.4. Mista Mwaniki ya jaddada cewa, “Wannan tsari zai tabbatar da moriyar kowa, ba kamar manufar da Donald Trump ya daukaka ta Cin Moriya daga Faduwar Wani ba.”

 

Ban da haka, jawabin da jakadan kasar Sin a Najeriya Yu Dunhai ya yi, a birnin Abuja a kwanan baya, ya zama mai goyon bayan maganganun da masanan kasashen Afirka suka fada, inda jakadan ya ce, ya kamata a kalli yakin ciniki a matsayin wata damar karfafa huldar hadin kai tsakanin kasashen Sin da Najeriya, gami da tsakanin Sin da kasashen Afirka baki daya. Yanzu kasashen Afirka na kokarin farfado da tattalin arzikinsu, saboda haka suna bukatar tsarin ciniki mai ‘yanci da ya shafi bangarori daban daban, da wani muhallin kasuwanci da ake iya hasashen yanayinsa na nan gaba. Yayin da kasar Sin a nata bangare take dukufa wajen bude kofarta ga kasashen ketare, da kokarin taimakon kasashen Afirka wajen raya kansu a kai a kai, matakan da ke da muhimmanci ga yunkurin saukaka yanayin rashin tabbas da ake fuskantar sakamakon yakin ciniki.

 

Sai dai wadanne matakai ne za a iya dauka don tinkarar yakin ciniki? Za mu iya ci gaba da daukar misalin kasar Lesotho, inda kayayyakin da take fitarwa kasar Amurka, idan Amurka ba ta so, to, za a iya bin shawarar Madam Ngozi Iweala, wadda ta ce sai a sayar da su ga sauran kasashen dake nahiyar Afirka. Ban da haka, kasar Lesotho za ta iya hadin gwiwa da kasar Sin wajen inganta tsarin masana’antu, ta yadda za ta lalubo sabuwar damar ciniki. Ganin yadda kasar Sin ta zama kasa ta farko da ta kulla huldar hadin kai bisa manyan tsare-tsare tare da Lesotho, kana adadin cinikin da ake yi tsakanin kasashen 2 ya riga ya karu zuwa dala miliyan 150 a bara.

 

Sinawa kan ce, “Dabara ta fi matsala yawa.” Mu yi kokarin tinkarar kalubale, ta yadda za a iya mayar da shi damar raya kai. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Za A Yi Jana’izar Fafaroma Francis A Ranar Asabar A Vatican

Next Post

Illolin Da Manufar Haraji Kan Kayayyaki Ta Haifar A Kan Amerikawa

Related

Sara Da Sassaka Ba Ya Hana Gamji Toho
Ra'ayi Riga

Sara Da Sassaka Ba Ya Hana Gamji Toho

12 hours ago
Raya Kasa Na Bukatar Bin Daidaitacciyar Hanya
Ra'ayi Riga

Raya Kasa Na Bukatar Bin Daidaitacciyar Hanya

2 days ago
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka
Ra'ayi Riga

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

1 week ago
Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci
Ra'ayi Riga

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

2 weeks ago
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

2 weeks ago
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

2 weeks ago
Next Post
Illolin Da Manufar Haraji Kan Kayayyaki Ta Haifar A Kan Amerikawa

Illolin Da Manufar Haraji Kan Kayayyaki Ta Haifar A Kan Amerikawa

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Tarwatsa Wuraren Haɗa Jabun Taki A Bauchi, An Cafke Mutum 5

‘Yansanda Sun Tarwatsa Wuraren Haɗa Jabun Taki A Bauchi, An Cafke Mutum 5

May 21, 2025
Kocin Super Eagle Ya Gayyaci Ahmed Musa Buga Gasar Kofin Unity A Landan

Kocin Super Eagle Ya Gayyaci Ahmed Musa Buga Gasar Kofin Unity A Landan

May 21, 2025
Farar Dabarar Da Tsoffin Masana’antu Ke Yi A Kasar Sin Don Tafiya Da Zamani

Farar Dabarar Da Tsoffin Masana’antu Ke Yi A Kasar Sin Don Tafiya Da Zamani

May 21, 2025
Tottenham Ta Doke Manchester United A Wasan Karshe Na Europa 

Tottenham Ta Doke Manchester United A Wasan Karshe Na Europa 

May 21, 2025
Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar ₦2.6bn

Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar ₦2.6bn

May 21, 2025
Shirye-shiryen Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista

Shirye-shiryen Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista

May 21, 2025
Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka

Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka

May 21, 2025
Sin Tana Da Karfi Wajen Tinkarar Hadari Da Kalubale A Fannoni Daban Daban

Sin Tana Da Karfi Wajen Tinkarar Hadari Da Kalubale A Fannoni Daban Daban

May 21, 2025
Sabbin Ministoci

Boko Haram: Majalisar Dattijai Ta Amince Da Kafa Sansanin Sojoji A Hong Ta Jihar Adamawa

May 21, 2025
Sin Ta Soki Yunkurin Amurka Na Hana Amfani Da Chips Kirar Kasar Sin

Sin Ta Soki Yunkurin Amurka Na Hana Amfani Da Chips Kirar Kasar Sin

May 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.