ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Na Ci Gaba Da Kokawa Kan Tsadar Iskar Gas

by Bello Hamza
2 years ago
Gas

‘Yan Nijeriya da dama na ci gaba da kokawa kan karin farashin iskar gas na LPG wanda ake amfani da shi wajen dafa abinci, duk da matakan da gwamnati ta dauka.

Wasu mazauna babban birnin tarayya Abuja, wadanda suka zanta da kamfanin dillancin labaran Nijeriya (NAN) a ranar Lahadi a Abuja, sun jaddada bukatar da yake akwai a kan gwamnati na ta gaggauta magance tsadar iskar gas din.

  • Maulidi: Fityanul Islam Ta Jajanta Wa Al’ummar Borno Kan Ibtila’in Ambaliyar Ruwa
  • Anya Barcelona Za Ta Iya Kai Bantenta Kuwa A Gasar Zakarun Turai Ta Bana?

Wannan a cewarsu zai taimaka wajen rage wasu kalubalen da ‘yan Nijeriya ke fuskanta.

ADVERTISEMENT

NAN ta ruwaito cewa ana siyar da duk kilogiram daya (1kg) na iskar gas a tsakanin N1,300 zuwa N1,400 ya danganta da wuri da zaka siya, kuma cika silinda mai nauyin kilogiram 12.5 a yanzu yana kai wa N16,000 zuwa N17,000 sabanin N12,500 zuwa N13,000 a watan Yuni da Yuli.

Idan dai za a iya tunawa, a watan Yuni da Yuli, iskar gas din ta ragu zuwa kasa zuwa naira 1,050 kan kowacce kilogiram, amma farashin ya karu a watannin da suka biyo.

LABARAI MASU NASABA

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

Rahoton Hukumar kididdiga ta kasa (NBS) na baya-bayan nan kan iskar gas na watan Yuli ya nuna cewa matsakaicin farashin dillalan iskar gas din kan silinda mai nauyin kilo 5 ya ragu da kashi 14.23 bisa dari a duk wata daga N6, 966.03 da aka samu a watan Yuni 2024 zuwa N5, 974.55 a watan Yuli 2024.

Haka kuma, matsakaicin farashin dillalan iskar gas na Silinda mai nauyin kilo 12.5 ya ragu da kashi 9.37 a kowanne wata daga N15, 736.27 a watan Yuni 2024 zuwa N14, 261.57 a watan Yulin 2024.

Wata ‘yar kasuwa kuma mahaifiyar ‘ya’ya uku Funke Bamidele ta ce karin kudin iskar gas din girki na daya daga cikin kalubalen da ‘yan Nijeriya ke fuskanta kasancewar shi ne tushen girki a gidaje da dama.

“Mun dauka farashin iskar gas din ya ragu a ‘yan watannin da suka gabata, sai muka sake farkawa zuwa wani karin.

“Iyalai da yawa suna amfani da iskar gas a gidajensu, kuma idan farashin ya ci gaba da karuwa, zai haifar da babban kalubale ga iyalai saboda da kyar muke iya tsira daga wannan mawuyacin halin da tattalin arziki ya fada.

“Man fetur yana da tsada, kananzir na da tsada, dizil yana da tsada, iskar gas yana da tsada. Ya ya gwamnati take son ‘yan Najeriya su rayu?

Gas
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tattalin Arziki

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

July 11, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Tattalin Arziki

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani
Tattalin Arziki

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
Next Post
Bishiyar Kuka Na Iya Kwashe Shekaru 2,000 A Raye

Bishiyar Kuka Na Iya Kwashe Shekaru 2,000 A Raye

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.