ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Na Ci Gaba Da Kokawa Kan Tsadar Iskar Gas

by Bello Hamza
2 years ago
Gas

‘Yan Nijeriya da dama na ci gaba da kokawa kan karin farashin iskar gas na LPG wanda ake amfani da shi wajen dafa abinci, duk da matakan da gwamnati ta dauka.

Wasu mazauna babban birnin tarayya Abuja, wadanda suka zanta da kamfanin dillancin labaran Nijeriya (NAN) a ranar Lahadi a Abuja, sun jaddada bukatar da yake akwai a kan gwamnati na ta gaggauta magance tsadar iskar gas din.

  • Maulidi: Fityanul Islam Ta Jajanta Wa Al’ummar Borno Kan Ibtila’in Ambaliyar Ruwa
  • Anya Barcelona Za Ta Iya Kai Bantenta Kuwa A Gasar Zakarun Turai Ta Bana?

Wannan a cewarsu zai taimaka wajen rage wasu kalubalen da ‘yan Nijeriya ke fuskanta.

ADVERTISEMENT

NAN ta ruwaito cewa ana siyar da duk kilogiram daya (1kg) na iskar gas a tsakanin N1,300 zuwa N1,400 ya danganta da wuri da zaka siya, kuma cika silinda mai nauyin kilogiram 12.5 a yanzu yana kai wa N16,000 zuwa N17,000 sabanin N12,500 zuwa N13,000 a watan Yuni da Yuli.

Idan dai za a iya tunawa, a watan Yuni da Yuli, iskar gas din ta ragu zuwa kasa zuwa naira 1,050 kan kowacce kilogiram, amma farashin ya karu a watannin da suka biyo.

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe

Rahoton Hukumar kididdiga ta kasa (NBS) na baya-bayan nan kan iskar gas na watan Yuli ya nuna cewa matsakaicin farashin dillalan iskar gas din kan silinda mai nauyin kilo 5 ya ragu da kashi 14.23 bisa dari a duk wata daga N6, 966.03 da aka samu a watan Yuni 2024 zuwa N5, 974.55 a watan Yuli 2024.

Haka kuma, matsakaicin farashin dillalan iskar gas na Silinda mai nauyin kilo 12.5 ya ragu da kashi 9.37 a kowanne wata daga N15, 736.27 a watan Yuni 2024 zuwa N14, 261.57 a watan Yulin 2024.

Wata ‘yar kasuwa kuma mahaifiyar ‘ya’ya uku Funke Bamidele ta ce karin kudin iskar gas din girki na daya daga cikin kalubalen da ‘yan Nijeriya ke fuskanta kasancewar shi ne tushen girki a gidaje da dama.

“Mun dauka farashin iskar gas din ya ragu a ‘yan watannin da suka gabata, sai muka sake farkawa zuwa wani karin.

“Iyalai da yawa suna amfani da iskar gas a gidajensu, kuma idan farashin ya ci gaba da karuwa, zai haifar da babban kalubale ga iyalai saboda da kyar muke iya tsira daga wannan mawuyacin halin da tattalin arziki ya fada.

“Man fetur yana da tsada, kananzir na da tsada, dizil yana da tsada, iskar gas yana da tsada. Ya ya gwamnati take son ‘yan Najeriya su rayu?

Gas
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja

MASU ALAKA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000
Tattalin Arziki

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
Tattalin Arziki

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe

May 29, 2026
Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
Tattalin Arziki

Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho

May 29, 2026
Next Post
Bishiyar Kuka Na Iya Kwashe Shekaru 2,000 A Raye

Bishiyar Kuka Na Iya Kwashe Shekaru 2,000 A Raye

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.