ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

 ‘Yan Ta’adda Na Neman ‘Yan Matan Indiya Da Tabar Wiwi Da Hodar Iblis A Matsayin Kudin Fansa

by Rabi'u Ali Indabawa
6 months ago
Wiwi

Kungiyar zamantakewa da siyasa ta kabilar Yarbawa, Afenifere, ta yi Allah-wadai da sabon yawaitar kutsen ‘yan ta’adda a yankin kudu maso yammacin Nigeria, tare da kira ga gwamnati da hukumomin tsaro da su kara kaimi wajen ceto yankin daga matsalar ‘yan bindiga.

A cikin wata sanarwar manema labarai da aka fitar a ranar Asabar, Sakataren Yada Labarai na kungiyar na kasa, Jare Ajayi, ya bayyana damuwar al’ummar Yarbawa kan yadda ake samun asarar rayukan jama’a kusan kullum a jihohi da dama.

  • Nijeriya Na Yunkurin Mayar Wa Da Manoman Tumatir Asarar Da Suka Yi Ta Naira Biliyan 1.3

Sun kuma yi nuni da yadda ake mummunar mu’amala da mutanen da aka sace, inda ake dukansu da wulakanta su ba tare da jin kai ba.

ADVERTISEMENT

Ajayi ya kawo misalai na hare-hare da dama, ciki har da: hare-hare kan coci-coci, ofisoshin ‘yan sanda, gidajen jama’a da manyan hanyoyi a Ondo, kore al’ummomi daga garuruwansu a Jihar Kwara, kisan manoma da kai hari kan matafiya a kan hanyar Igbeti–Kisi a yankin Oke-Ogun na Jihar Oyo, da kuma munanan sace-sacen mutane a Jihar Ekiti, inda aka kashe wasu daga cikin wadanda aka sace sannan aka rike gawarwakinsu domin neman kudin fansa.

Kudin Fansa

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

Ya kara da cewa: “Babbar shaida ta rashin tausayi da mugunta na wadannan miyagu ita ce yadda suka nemi Naira miliyan 1.5, tabar wiwi (Indian hemp), hodar iblis (cocaine), wani maganin maye na roba da ake kira ICE, da kuma kwandunan giyar kwalba, domin a sako gawar wani mutum da ke hannunsu.”

Ya ci gaba da cewa masu garkuwa da mutanen har ma sun bukaci a kawo musu ‘yan mata budurwai a matsayin fansa domin su saki maza hudu da suka sace a baya.

A cewar Sakataren Yada Labarai na Afenifere, Jare Ajayi: “Har zuwa kwanan nan, ana kallon gida a matsayin mafaka mai aminci. Abin takaici, hakan ba haka yake ba yanzu. Wasu ma’aurata an kai musu hari a gaban gidansu a Akure, a Jihar Ondo, inda aka harbi mijin yayin da yake kokarin hana sace matarsa.”

Ajayi ya kuma bayyana cewa Elder Igwe, mahaifin tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Ebonyi, an sace shi ne yayin da yake kan hanyarsa ta zuwa coci a ranar Lahadi, 1 ga Maris.

Haka kuma a Erinmope-Ekiti da ke Jihar Ekiti, an sace iyali guda mai mutum biyar da misalin karfe 7 na yamma, a lokacin da mutane suke sallar magariba a masallaci.

Ajayi ya kara lura cewa irin wadannan hare-hare na dogon lokaci ana samun su a jihohi da dama, ciki har da Jihohin Kwara, Filato, Binuwe, Borno, Kebbi, Nasarawa, Neja, Katsina, da Jihar Kaduna.

Ya kuma ce ’yan gudun hijira da suka dawo daga Kamaru su ma sun fada cikin irin wadannan hare-hare a Jihar Bauchi.

Da yake tuna wani lamari da ya faru a Jihar Edo, Sakataren Yada Labarai na Afenifere, Jare Ajayi, ya bayyana yadda masu garkuwa da mutane suka sace wani likita da dan’uwansa, inda suka kashe kanin amma suka saki likitan bayan an biya kudin fansa.

Ajayi ya ce: “Lokacin da ’yar daya daga cikin masu garkuwar ta kamu da rashin lafiya, likitan wanda ke bakin aiki a asibiti ya gane mutanen da suka aikata laifin, sannan ya sanar da ‘yansanda, lamarin da ya kai ga kama su.”

Ya kara da cewa: “Abin lura a nan shi ne cewa dan bindigar ya daraja rayuwar ‘yarsa har ya kai ta asibiti domin a kula da lafiyarta, amma a lokaci guda bai ga laifi ba wajen kashe rayukan wasu mutane.”

Ajayi ya jaddada cewa ta’addanci da sace mutane sun yawaita sosai, amma ya ce matsalar ba wadda ba za a iya shawo kanta ba ce, yana mai cewa:

“‘Yan bindiga ba aljanu ba ne kuma ba su da karfin da ba za a iya kayar da su ba.”

Daga nan ya yi kira ga a dauki mataki mai karfi domin katse hanyoyin da ‘yan bindiga ke samun kudi, wadanda suka hada da:

Wasu attajirai marasa gaskiya, kungiyoyin gida da na kasa da kasa, wasu jami’an gwamnati, al’ummomin da ke biyan kudin kariya ko kudin girbi, kudin fansa daga wadanda aka sace, da kuma sata kai tsaye.

Masu Hakar Ma’adanan Kasar Waje

Ya kuma yi kira a gudanar da bincike kan ’yan waje da ke da hannu a cikin harkokin hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba, wadanda ka iya zama suna jawo korar al’ummomi daga garuruwansu.

“Bayanan da aka samu daga ’yan bindiga da aka kama kuma aka gurfanar da su sun nuna cewa suna da masu daukar nauyi. Saboda haka, yana da muhimmanci a bi diddigin masu daukar nauyin da masu shiga tsakani, katse hanyoyin samun kudade da makamai, kai farmaki a dazuzzukan da suke boye, magance cin hanci da barnar da ke cikin hukumomin tsaro, karfafa ma’aikata, da tabbatar da kafa ‘yan sanda na jiha nan da nan,” in ji Ajayi.

Afenifere ta yaba wa Shugaba Bola Tinubu saboda jajircewarsa wajen ci gaba da kafa ‘yan sanda na jiha, tana mai jaddada kira da ya yi ga Majalisar Kasa da ta hanzarta gyara kundin tsarin mulki don tabbatar da fara aiki nan take.

Haka kuma an yabi sabon Sufeto Janar din ‘yansanda, Tunji Disu saboda kafa kwamitin da zai tsara hanyoyin da za a yi amfani da su wajen tura ‘yan sanda na jiha.

Kungiyar ta sake jaddada kiranta ga gwamnonin kudu maso yamma da su aiwatar da matakai na kai farmaki a boyayyun wuraren ‘yan bindiga, kula da yankunan da suka fi fuskantar barazana, da hadin kai sosai da Gwamnatin Tarayya domin tabbatar da kafa ‘yan sanda na jiha cikin gaggawa a jihohinsu.

 

Wiwi
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Next Post
Yadda Aka Bar Iyakokin Nijeriya 1,978 Babu Jami’an Tsaro

Yadda Aka Bar Iyakokin Nijeriya 1,978 Babu Jami’an Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.